• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Jarumai Ne Suka Samu Kyautukan Motoci?

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Jarumai

A makon da ya gabata hotuna da ma bidiyoyi suka yadu a kafafen sada zumunta musamman manhajar Facebook inda aka ga babban mataimki na musamman akan harkokin nishadi na gwamnan Jihar Kano Malam Tijjani Gandu ya na raba makullan mota da kudade ga wasu daga cikin jarumai a masana’antar Kannywood.

Kamar yadda aka gani a cikin faifan bidiyon an ga Tijjani ya na mika makullan mota ga jaruman tare da leda wadda ya ce ta na dauke da kudaden da za su yi amfani da su wajen sayen man fetur da kuma yi wa motocin rijista da hukumar kiyayaye hadurra ta Nijeriya, inda kuma ya ce wannan kyauta ce daga Gwamnan Jihar Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya ce abasu domin nuna godiya a kan jajircewarsu a lokacin yakin neman zaben jihar Kano da aka gudanar a shekarar 2023.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Xi Ya Bukaci A Yi Kokarin Tafiyar Da Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Yadda Ya Kamata

Yayin da wasu ke fita daga tsagin Kwankwasiyya na siyasar Jihar Kano su na komawa tsagin APC ta hannun mataimakin shugaban majalisar Dattawa Sanata Barau Jibrin (Maliya) su kuma wadanda suka jure suka tsaya a jam’iyar NNPP mai alamar littafi suke rabauta da kyaututtukan manyan motoci masu tsada da kuma kudade daga gwamnatin jihar ta Kano, inda babban mai taimakawa gwamnan akan harkokin nishadi Malam Tijjani Gandu ya ce gwamnan ya matukar yaba wa da irin gudunmawar da jaruman suka ba shi a lokacin da yake yakin neman zaben gwamna.

Hakan ya sa gwamnan ya yi amfani da kalmar bahaushe da ta ce yaba kyauta tukwuici, ta hanyar gwangwaje wasu daga cikin jarumai mata da maza da motoci da kuma kudaden shan mai, Tijjani kuma ya tabbatar da cewar wannan somin tabi ne domin kuwa gwamna Abba Kabir Yusuf ya na sane da wadanda suka samu da wadanda basu samu ba,da sannu sanu duk wanda ya cancanci samun kyautar mota daga hanun gwamnan za ta shigo hannunshi inji shi.

Leadership Hausa ta kalato maku sunayen jaruman Kannywood da suka samu wannan kyauta ta mota daga gwamnan Jihar Kano Eng Abba Kabir Yusuf ta hannun babban mai taimaka masa akan harkokin nishadi Malam Tijjani Gandu, ga sunayen kamar haka, Alasan Kwalle, Bashir Nayaya, Baba Sogiji, Isiyaku Jalingo a bangaren maza sai kuma Ainau Ade da Yahanasu Sani a bangaren mata.

LABARAI MASU NASABA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala
Nishadi

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Next Post
Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

LABARAI MASU NASABA

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.