• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Jarumai Ne Suka Samu Kyautukan Motoci?

by Rabilu Sanusi Bena
8 months ago
in Nishadi
0
Wadanne Jarumai Ne Suka Samu Kyautukan Motoci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata hotuna da ma bidiyoyi suka yadu a kafafen sada zumunta musamman manhajar Facebook inda aka ga babban mataimki na musamman akan harkokin nishadi na gwamnan Jihar Kano Malam Tijjani Gandu ya na raba makullan mota da kudade ga wasu daga cikin jarumai a masana’antar Kannywood.

Kamar yadda aka gani a cikin faifan bidiyon an ga Tijjani ya na mika makullan mota ga jaruman tare da leda wadda ya ce ta na dauke da kudaden da za su yi amfani da su wajen sayen man fetur da kuma yi wa motocin rijista da hukumar kiyayaye hadurra ta Nijeriya, inda kuma ya ce wannan kyauta ce daga Gwamnan Jihar Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya ce abasu domin nuna godiya a kan jajircewarsu a lokacin yakin neman zaben jihar Kano da aka gudanar a shekarar 2023.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Xi Ya Bukaci A Yi Kokarin Tafiyar Da Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Yadda Ya Kamata

Yayin da wasu ke fita daga tsagin Kwankwasiyya na siyasar Jihar Kano su na komawa tsagin APC ta hannun mataimakin shugaban majalisar Dattawa Sanata Barau Jibrin (Maliya) su kuma wadanda suka jure suka tsaya a jam’iyar NNPP mai alamar littafi suke rabauta da kyaututtukan manyan motoci masu tsada da kuma kudade daga gwamnatin jihar ta Kano, inda babban mai taimakawa gwamnan akan harkokin nishadi Malam Tijjani Gandu ya ce gwamnan ya matukar yaba wa da irin gudunmawar da jaruman suka ba shi a lokacin da yake yakin neman zaben gwamna.

Hakan ya sa gwamnan ya yi amfani da kalmar bahaushe da ta ce yaba kyauta tukwuici, ta hanyar gwangwaje wasu daga cikin jarumai mata da maza da motoci da kuma kudaden shan mai, Tijjani kuma ya tabbatar da cewar wannan somin tabi ne domin kuwa gwamna Abba Kabir Yusuf ya na sane da wadanda suka samu da wadanda basu samu ba,da sannu sanu duk wanda ya cancanci samun kyautar mota daga hanun gwamnan za ta shigo hannunshi inji shi.

Leadership Hausa ta kalato maku sunayen jaruman Kannywood da suka samu wannan kyauta ta mota daga gwamnan Jihar Kano Eng Abba Kabir Yusuf ta hannun babban mai taimaka masa akan harkokin nishadi Malam Tijjani Gandu, ga sunayen kamar haka, Alasan Kwalle, Bashir Nayaya, Baba Sogiji, Isiyaku Jalingo a bangaren maza sai kuma Ainau Ade da Yahanasu Sani a bangaren mata.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GwamnaJarumaiMotoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata A Magance Shigar Banza A Masana’antar Kannywood -Samha M Inuwa

Next Post

Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

Related

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

2 days ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

2 days ago
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

1 week ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

2 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

2 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

3 weeks ago
Next Post
Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.