ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Jarumai Ne Suka Samu Kyautukan Motoci?

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Jarumai

A makon da ya gabata hotuna da ma bidiyoyi suka yadu a kafafen sada zumunta musamman manhajar Facebook inda aka ga babban mataimki na musamman akan harkokin nishadi na gwamnan Jihar Kano Malam Tijjani Gandu ya na raba makullan mota da kudade ga wasu daga cikin jarumai a masana’antar Kannywood.

Kamar yadda aka gani a cikin faifan bidiyon an ga Tijjani ya na mika makullan mota ga jaruman tare da leda wadda ya ce ta na dauke da kudaden da za su yi amfani da su wajen sayen man fetur da kuma yi wa motocin rijista da hukumar kiyayaye hadurra ta Nijeriya, inda kuma ya ce wannan kyauta ce daga Gwamnan Jihar Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya ce abasu domin nuna godiya a kan jajircewarsu a lokacin yakin neman zaben jihar Kano da aka gudanar a shekarar 2023.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Xi Ya Bukaci A Yi Kokarin Tafiyar Da Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Yadda Ya Kamata

Yayin da wasu ke fita daga tsagin Kwankwasiyya na siyasar Jihar Kano su na komawa tsagin APC ta hannun mataimakin shugaban majalisar Dattawa Sanata Barau Jibrin (Maliya) su kuma wadanda suka jure suka tsaya a jam’iyar NNPP mai alamar littafi suke rabauta da kyaututtukan manyan motoci masu tsada da kuma kudade daga gwamnatin jihar ta Kano, inda babban mai taimakawa gwamnan akan harkokin nishadi Malam Tijjani Gandu ya ce gwamnan ya matukar yaba wa da irin gudunmawar da jaruman suka ba shi a lokacin da yake yakin neman zaben gwamna.

ADVERTISEMENT

Hakan ya sa gwamnan ya yi amfani da kalmar bahaushe da ta ce yaba kyauta tukwuici, ta hanyar gwangwaje wasu daga cikin jarumai mata da maza da motoci da kuma kudaden shan mai, Tijjani kuma ya tabbatar da cewar wannan somin tabi ne domin kuwa gwamna Abba Kabir Yusuf ya na sane da wadanda suka samu da wadanda basu samu ba,da sannu sanu duk wanda ya cancanci samun kyautar mota daga hanun gwamnan za ta shigo hannunshi inji shi.

Leadership Hausa ta kalato maku sunayen jaruman Kannywood da suka samu wannan kyauta ta mota daga gwamnan Jihar Kano Eng Abba Kabir Yusuf ta hannun babban mai taimaka masa akan harkokin nishadi Malam Tijjani Gandu, ga sunayen kamar haka, Alasan Kwalle, Bashir Nayaya, Baba Sogiji, Isiyaku Jalingo a bangaren maza sai kuma Ainau Ade da Yahanasu Sani a bangaren mata.

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Jarumai
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.