• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakatarorin tsaron Amurka da na Rasha sun tattauna ta wayar tarho, a wani yunkuri na ba kasafai ake mu’amala ba tsakanin kasashen biyu tun bayan da Rasha ta mamaye Ukraine.

Sakataren tsaron Amurka, Lloyd Austin da takwaransa na Rasha Sergei Shoigu sun gana ne a ranar Juma’a, kamar yadda kasashen biyu suka tabbatar.

  • Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)
  • DA DUMI-DUMI: An Sanya Wa ‘Yan Nijeriya Dokar Hana Samun Izinin Shiga Dubai

Bangarorin biyu sun ce an tattauna ne kan halin da ake ciki a Ukraine.

Wannan dai shi ne karo na farko da kasashen biyu suka bayar da bayanin wata tattaunawa tun ranar 13 ga Mayu 2022.

Bayan tattaunawar ta ranar Juma’a, ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta ce Mista Austin “ya jaddada muhimmancin kiyaye layukan sadarwa a Ukraine”.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ma’aikatar tsaron Rasha kuwa ta ce “an tattauna batutuwan da suka shafi tsaron kasa da kasa ciki har da halin da ake ciki a Ukraine”.

Bayan tattaunawar da suka yi a baya a watan Mayu, Mista Austin ya bukaci takwaransa da ya kira tsagaita bude wuta cikin gaggawa, ko da yake Amurka ba ta ambaci bukatar ba a wannan karon.

Hakan dai na zuwa ne bayan da shugaban Kasar Rasha, Vladimir Putin ya bayyana cewa watakila a shirye yake ya yi amfani da makaman nukiliya a Ukraine, da kuma gargadin da shugaban Amurka Joe Biden ya yi.

Hukumomin Amurka da Birtaniya sun ce sun yi imanin cewa yiwuwar Mista Putin na aiwatar da wadannan barazanar babu tabbas.

Rikicin da ya yi tsami tsakanin Amurka da Rasha ya kara tabarbarewa tun bayan mamayar Ukraine.

Shugabannin kasashen biyu sun yi wata ganawa a tsakiyar shekarar 2021, wanda aka bayyana a matsayin wani mataki mai kyau na kyautata alaka.

Amma wannan ci gaban ya tsaya bayan da tashe-tashen hankula suka yi kamari a Ukraine.

Tun bayan mamayar dai babu wata tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen Amurka da Rasha.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJoe BidenMamayaRashaUkraineVladimir PutinYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)

Next Post

Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

7 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

9 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

14 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

14 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

18 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

1 day ago
Next Post
Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.