• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Kasar Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Daina Tsoma Bakin Soja Ba Bisa Ka’ida Ba A Syria

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Kasar Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Daina Tsoma Bakin Soja Ba Bisa Ka’ida Ba A Syria
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin zaman taro na 51 na kwamitin kare hakkin dan-Adam, wakilin kasar Sin a kwamitin kare hakkin dan-Adam na MDD minista Jiang Duan ya yi Allah wadai da katsalandan din sojan da ya saba da doka da Amurka ta yi a kasar Syria.

Mr. Jiang Duan ya nuna cewa, matakin soja na Amurka ya keta muhimman hakkokin bil-adama na al’ummar Syria, don haka, ya bukaci kasar Amurka da ta gaggauta dakatar da take hakkin bil-Adam da take yi.

  • Matakan Soja Na Amurka Sun Jefa Wasu Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Matsala

Jiang Duan ya bayyana cewa, an shafe fiye da shekaru goma ana jinkirta batun kasar Syria, kuma har yanzu al’ummar kasar na fama da talauci da yaki. Kuma alhakin hakan ya rataya ne a wuyan Amurka da sauran kasashen yammacin duniya.

Kasar Amurka dai ta sha kaddamar da hare-haren soji a kasar Syria, lamarin da ya sabbaba hasarar rayukan fararen hula da matsugunai a Syria, tare da haddasa asarar dukiyoyi da ba za a iya misaltawa ba.

A watan da ya gabata ne sojojin Amurka suka kaddamar da wani sabon farmaki ta sama a gabashin kasar Syria, wanda ya ci gaba da keta hurumin kasar tare da kara ta’azzara wahalhalun da al’ummar Syria ke fama da shi.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Bugu da kari, kasar Amurka ta kakkaba wa kasar Syria wasu matakai na tilastawa, wadanda suka saba doka, lamarin da ya sa al’ummar kasar wahalar samun zaman lafiya na yau da kullum, kuma matakan raya tattalin arziki da sake gina kasar, duk suna fuskantar matsaloli.

Har zuwa wannan lokaci, sojojin kasar Amurka ne ke da iko kan rijiyoyin man fetur, da iskar gas da sauran albarkatun kasar, inda suka mamaye manyan yankunan kasar da ake hako mai, tare da kwashe sama da kashi 80 cikin 100 na yawan man da ake hakowa a kasar, suna kuma fasa kwauri da lalata hatsin da kasar Syria ta adana, hakan ya keta ’yancin al’ummar kasar na samun abinci, da lafiya, da bunkasuwa, da sauran muhimman hakkoki na bil-Adama matuka.

Jiang Duan ya ce, rikicin kasar Syria ya nuna cewa, tsoma baki na kasashen waje, da tsokana, da matsin lamba, da sanya takunkumai, ko kadan ba za su taimaka wajen warware matsalar ba. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakarun Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya

Next Post

Wang Yi Ya Zanta Da Sakataren Wajen Amurka

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

6 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

6 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

7 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

9 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

10 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

11 hours ago
Next Post
Wang Yi Ya Zanta Da Sakataren Wajen Amurka

Wang Yi Ya Zanta Da Sakataren Wajen Amurka

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.