• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Irin Hadin Kai Ne Afirka Ke Bukata?

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Wane Irin Hadin Kai Ne Afirka Ke Bukata?

DCIM100MEDIA

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau na ga wata kasida da dan jaridar Najeriya David Hundeyin ya rubuta, wadda aka wallafa a shafin yanar gizon ” Guancha.cn” na kasar Sin. Cikin kasidar ya ambaci “salon tattalin arziki mafi kyau” da kasashen yamma suka zaba wa kasashen Afirka.

 

Hundeyin ya ce, wannan tsari na tattalin arziki ya ba nahiyar Afirka damar samar da albarkatun kasa masu araha kawai, wadanda ba a sarrafa su ba, da kuma shuke-shuken da ba za a iya ci ba, kuma da zarar an hako wadannan albarkatun kasa da kuma samar da su, dole ne a fitar da su zuwa kasashen waje cikin sauki da sauri, don kayyade kudin da ake kashewa wajen gudanar da masana’antu.

  • Firaministan Sin Ya Taya Murnar Bude Taron Hukumar IAEA Karo Na 68
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Bai Wa Maiduguri Tallafin Dala Miliyan 6

Mista Hundeyin ya ba da misali da kasar Amurka, inda ya ambaci yadda Amurka ke shirin zuba jarin dalar Amurka biliyan 10 a aikin ginin layin dogo mai suna “Lobito Corridor”, a kasashe irin su Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo da Angola. A cewarsa, ko da yake wani sabon aiki ne, amma tunanin zuba jari bai taba canzawa ba. Ya ce, wannan layin dogo bai shigar da ma’adinan Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo zuwa yankunan da suka fi samun hadewar tattalin arziki da ababen more rayuwa masu inganci a gabashin Afirka ba, maimakon haka, an karkata zuwa yamma ta yadda za a ratsa kungurmin dajin kasar Angola, wanda fadinsa ya kai fiye da kilomita 1000. Duk da cewa layin dogon “kusan babu wata mu’ammala mai ma’ana tare da cibiyoyin masana’antu ko na jama’a na kasashen Afirka,” wanda a zahiri ya bayyana niyyar jigilar ma’adinan kasashen Afirka daga wuraren hakar ma’adinai zuwa tashar jiragen ruwa mafi kusa da kasar Amurka da wuri-wuri, gami da kokarin magance cudanya da jama’ar wuraren.

 

Labarai Masu Nasaba

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

A cewar Hundeyin, idan aka kwatanta da tsarin hadin gwiwar kasashen yamma da Afirka, abin da kasar Sin ke yi ya sha bamban. Misali, dimbin gine-ginen da kamfanonin kasar Sin suka aiwatar a Kilamba, wani yanki dake dab da Luanda, fadar mulkin Angola, ya zama babban misali da aka samu na fadada biranen Afirka cikin tsari. Ban da haka kuma, yankin masana’antu da kasar Sin ta zuba jari da kuma ginawa a Angola, zai aza harsashi ga aikin raya masana’antun sarrafa saholami a Angola, da samarwa kasar da guraben aikin yi har 12,000, da kuma kudin shiga har dalar Amurka miliyan 400 a duk shekara.

 

A ra’ayin Hundeyin, bambancin da ke tsakanin tsarin Sin da kasashen yamma na shiga cikin harkokin tattalin arzikin Afirka shi ne, kasar Sin tana neman cin riba tare da kokarin tabbatar da adalci, yayin da kasashen yamma suka kasance masu girman kai da kwadayi, kuma da alama ba su da damar samun ingantuwa ko ci gaba game da hakan. Ya ce, “Nasarar da kasar Sin ta samu a fannin samar da tasiri a nahiyar Afirka na nuni da cewa, za a iya tabbatar da moriyar dukkan bangarori a hadin gwiwar tattalin arziki da ta cinikayya, yayin da layin dogo na Lobito ya nuna kurakuran manufar kasar Amurka kan kasashen Afirka.”

 

Tabbas, Hundeyin ya bayyana ra’ayinsa ne. Sai dai wani abu da ba za a iya musantawa ba shi ne, hadin gwiwar Sin da Afirka ya kawo sauye-sauye a fannin hadin gwiwa da kasashen waje ke yi da kasashen Afirka, inda aka baiwa kasashen Afirka damar zabar ayyukan hadin gwiwar da suke bukata, wadanda za su iya haifar da ci gaba.

 

To, wane irin hadin kai ne kasashen Afirka suke bukata a hakika? Muna iya yin la’akari da shawarwarin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gabatar game da hadin gwiwar kasa da kasa da Afirka a gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da aka yi a nan birnin Beijing a farkon wannan wata, wato su ne:

Na farko, nacewa kan adalci. Samun zamanantarwa ba hakkin wasu ‘yan tsirarrun kasashe ba ne, kuma dole ne a tabbatar da ‘yancin ci gaban kasashen Afirka.

Na biyu, tabbatar da daidaito. Dole ne a mutunta bukatun Afirka da ‘yancin mutanen Afirka na neman hanyoyin raya kasa na kansu.

Na uku, neman hakikanin sakamako. Ya kamata a yi kokarin cika alkawari, maimakon wasa da fatar baki.

 

Ina ganin cewa, ko wane ne, ko wane irin hadin kai ne, idan har da gaske za a iya cimma wadannan abubuwa guda uku na sama, to, wannan aboki ya cancanci a yi hadin gwiwa da shi. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Sanya Takunkumi Kan Kamfanonin Sojan Amurka Wadanda Suka Sayar Da Makamai Ga Yankin Taiwan

Next Post

Za A ‘Yantar Da Falasɗinawa Nan Ba Da Jimawa Ba – Fani-Kayode

Related

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

1 day ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

2 days ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

5 days ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

1 week ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

2 weeks ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

2 weeks ago
Next Post
Gaza

Za A 'Yantar Da Falasɗinawa Nan Ba Da Jimawa Ba - Fani-Kayode

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.