ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Tsaro

Shugaban majalisar kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afirka ta ECOWAS Omar Touray, ya bayyana a kwanan baya cewa, yanayin tsaro a yammacin Afirka na tabarbarewa cikin sauri, har ma ya riga ya kai wani matsayi na ta-baci.

A ganin ECOWAS din, wani babban dalilin da ya haddasa hakan shi ne rashin kwanciyar hankali a wasu kasashe. Misali, juyin mulki da bai samu nasara ba a kasar Benin, na ranar 7 ga watan da muke ciki, da juyin mulki da sojojin kasar Guinea-Bissau suka yi a karshen watan da ya gabata. Hakika bisa alkaluman da wasu kafofin watsa labarai suka gabatar, an ce cikin shekaru fiye da 10 da suka wuce, an samu aukuwar juyin mulki, ko kuma yunkurin kifar da gwamnati da bai yi nasara ba, a rabin kasashe mambobin kungiyar ECOWAS, ciki har da juyin mulki da aka yi a kasashen Mali, da Burkina Faso, da Nijar, tsakanin shekarar 2020 da 2023. Kana bayan da sojojin kasashen 3 sun kwace ragamar mulki, an fara samun tsamin dangantaka tsakanin wadannan kasashen da kungiyar ECOWAS, lamarin da ya sanya kasashen janye jiki daga ECOWAS a watan Janairun bana, tare da kafa kungiyar hadin gwiwar kasashen yankin Sahel ta AES.

Ban da haka, hare-haren ta’addanci su ma suna haifar da tashin hankali a yammacin Afirka. Bisa wani rahoto da cibiyar nazarin tattalin arziki da zaman lafiya ta kasar Australiya ta fitar, an ce cikin kasashe 10 da suka fi fama da hare-haren ta’addanci a bara, 5 suna yankin yammacin Afirka da na Sahel, inda adadin hare-haren ta’addanci da suka auku a yankin ya kai kaso 19% na adadin duniya, kana yawan mutanen da suka rasa rayuka a yankin sakamakon ta’addanci, ya kai kaso 51% cikin jimillar na duniya. Haka zalika, an ce a bana, a Najeriya kadai, kungiyoyin ’yan ta’adda irinsu ISWAP, da Boko Haram, sun kaddamar da hare-hare fiye da 300. Inda ayyukan ta’addanci suka haifar da bazuwar makamai, da rashin tsari da oda, a kauyuka da kananan hukumomi, lamarin da ya ba ’yan fashin daji karin damammakin tayar da zaune-tsaye.

ADVERTISEMENT

Yanzu haka a jihar Zamfara ta Najeriya, hare-haren ’yan fashin daji sun lalata yanayin rayuwar dimbin mutane mazauna kauyuka, da tilastawa dubun-dubatar mutane kama hanyar gudun hijira, yayin da tashin hankali ke ci gaba da bazuwa zuwa jihohin makwabta irinsu Sokoto, da Kebbi, da Kaduna, da dai sauransu.

To, ko ta yaya kasashen yammacin Afirka za su iya tinkarar matsalar tsaro? Dangane da wannan tambaya, shahararren masanin ilimin siyasa na kasar Ghana Paul Frimpong, ya bayar da shawarar a nemi amsa daga shawarar tabbatar da tsaron duniya ta (GSI) wadda kasar Sin ta gabatar.

LABARAI MASU NASABA

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Wannan shawara ta Sin ta jaddada muhimmancin tabbatar da tsaro na bai daya mai dorewa, bisa hadin gwiwar bangarori daban daban, da mayar da hankali kan damuwar duk wata kasa, da girmama mulkin kai, da neman daidaita rikici da ayyukan ta’addanci ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa. A ganin Mista Frimpong, shawarar GSI da kasar Sin ta gabatar tana iya ba da taimako wajen kawar da sabanin ra’ayin da ake samu tsakanin kungiyoyin ECOWAS da AES, da kulla alaka mai karfi ta hadin kai a tsakanin kasashen yammacin Afirka, ta fuskar dakile ta’addanci da tabbatar da kwanciyar hankali.

Hakika matukar an yi hadin kai, to, tabbas hakan zai haifar da sakamako. Misali, daga watan Maris na shekarar 2024 zuwa watan Yuli na shekarar 2025, kasashen Najeriya, da Nijar da Chadi, sun dauki matakin soja na hadin gwiwa, mai taken “Garkuwar Sahel”, don yaki da kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi, inda aka kashe ’yan ta’adda fiye da 1200, ciki har da madugansu fiye da 80, da rushe maboyar ’yan ta’adda 37, tare da rage yawan laifukan sace mutane dake aukuwa a kan iyakar kasashen 3 da kaso 40%. Ban da haka, a yayin da ake tinkarar yunkurin juyin mulki a kasar Benin a kwanakin nan, tallafin soja da Najeriya da sauran mambobin kungiyar ECOWAS suka bayar, shi ma ya taka muhimmiyar rawa wajen maido da kwanciyar hankali a kasar Benin.

Sa’an nan kasashen yammacin Afirka, su ma za su iya hadin gwiwa da kasashen dake wajen nahiyar, misali kasar Sin. A wajen wani taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, kan batun yaki da ta’addanci a yammacin Afirka da yankin Sahel, wanda ya gudana a watan da ya gabata, wakilin kasar Sin ya yi alkawarin cewa, Sin tana tsayawa tsayin daka wajen nuna cikakken goyon baya ga kasashen Afirka, a fannin wanzar da zaman lafiya da tsaro, kuma za ta karfafa hadin gwiwarta da yammacin Afirka, da yankin Sahel ta fuskar dakile ta’addanci, don samar da karin gudunmowar kare zaman lafiya da tsaro a yankunan, gami da a duk nahiyar Afirka gaba daya.

Hausawa su kan ce, tsintsiya daya ba ta shara. Tabbas, shawarar GSI da kasar Sin ta gabatar, ita ma ta nuna irin wannan ra’ayi. Muna fatan ganin kasashen yammacin Afirka sun karfafa hadin kansu, da kokarin hadin gwiwa da abokan hulda na sauran sassan duniya, ta yadda za su iya cimma burinsu na tabbatar da tsaro, da kwanciyar hankali a yankin da suke ciki. (Bello Wang)

Tsaro
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah
  • Sulaiman
    An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

MASU ALAKA

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”
Ra'ayi Riga

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Next Post
Bunkasar Masana’antun Kasar Sin Ya Kai Kaso 6.0% a Watanni 11 Na Farkon Shekarar Bana

Bunkasar Masana'antun Kasar Sin Ya Kai Kaso 6.0% a Watanni 11 Na Farkon Shekarar Bana

LABARAI MASU NASABA

Hisbah

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026
An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

July 22, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

July 22, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

July 22, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.