ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Beijing

A kwanakin baya, dusar kankara ta sauka a birnin Beijing a karon farko tun bayan da aka shiga lokacin hunturu na bana. Dusar kankara ta kara kawata birnin, sai dai ta haifar da matsala ga zirga-zirgar mazauna birnin. A baya, bayan saukar dusar kankara, a kan yi amfani da sinadaran narkar da kankara wajen kawar da kankarar da ta mamaye hanyoyi. Amma a wannan shekara, an fara kayyade yin amfani da sinadaran narkar da kankara a birnin Beijing, kuma a maimakon hakan, mahukuntan birnin sun kara tura ma’aikata da motocin kawar da kankara da sauran na’urori don gudanar da aikin.

Dalilin da ya sa aka kayyade yin amfani da sinadaran narkar da kankara a birnin Beijing shi ne, don neman rage illolin da hakan ka iya haifarwa muhalli. An ce, sinadaran narkar da kankara su kan kunshi potassium chloride, da sodium chloride, wadanda in sun hadu da kankara, suna iya rage sanyin digirin daskararren ruwa har zuwa kasa da sifiri, ta yadda kankara za ta narke nan da nan zuwa ruwa. Amma a sa’i daya, sinadaran na iya haifar da illoli ga hanyoyi da muhalli, har da lafiyar jikin dan Adam. Misali, in ruwan da ke kunshe da sinadaran ya shiga cikin kasa, zai iya gurbata ruwan da ke karkashin kasa, wanda hakan ke haifar da barazana ga ingancin ruwan sha da ma muhallin rayuwar dabbobi da tsirrai.

Yadda aka kayyade yin amfani da sinadaran narkar da kankara, ya shaida yadda manufar kiyaye muhalli ke zame wa al’ummar kasar Sin jini da tsoka. A hakika, in mun lura, karin motoci masu amfani da makamashi mai tsabta na kara fitowa a titunan kasar Sin cikin ‘yan shekarun baya, kuma dazuzzukan da aka dasa sun kara yawaita, ga kuma iska da ruwan koguna na kara tsabta. Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, cikin shekaru biyar da suka gabata, kasar Sin ta gaggauta raya nau’o’in makamashi masu tsabta, har ma ta kai ga kafa tsarin samar da makamashi masu tsabta mafi girma a duniya, kuma yawan wutar lantarki da ta iya samarwa ta amfani da makamashi masu tsabta ya karu da kimanin kaso 60%. Baya ga haka, yawan ranakun da ake samun iska mai inganci a biranen kasar cikin shekara ya kiyaye matsayin kaso 87%, kuma fadin dazuzzukan kasar ma ya karu da kaso 2%, lamarin da ya sa kasar Sin ta zama kasar da ta fi saurin karuwar dazuzzuka a fadin duniya.

ADVERTISEMENT

A hakika, tabbatar da ci gaban kasa ba tare da gurbata muhalli ba, manufa ce da kasar Sin ke tsayawa tsayin daka a kai. Idan ba a manta ba, cikakken zama na hudu na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 20 da aka gudanar a watan Oktoban bana, ya bukaci a gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki, da zaman al’umma ya zama irin na kiyaye muhalli, tare da gina kyakkyawar kasar Sin. Sai kuma a kwanakin baya, mahukuntan kasar Sin sun kira babban taro na tattauna aikin raya tattalin arzikin kasar, inda aka sanya “burikan kaiwa kololuwar fitar da hayakin carbon da kawar da tasirinsa, da kuma kara azamar ingiza sauya akala zuwa ci gaba ba tare da gurbata yanayi ba” a matsayin wani muhimmin aikin da za a gudanar wajen raya tattalin arziki a shekara mai zuwa.

Burikan da aka gabatar sun shaida niyyar kasar Sin ta tabbatar da bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba. A yayin da ake fuskantar matsalar karancin makamashi, da kuma kalubalen sauyin yanayi a fadin duniya, manufar kasar Sin ta tabbatar da bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba tana da muhimmiyar ma’ana ga duniya. Sabo da na farko, kasancewar kasar Sin kasa mai tasowa mafi girma a duniya, tabbatar da bunkasuwarta ba tare da gurbata muhalli ba zai yi matukar taimakawa wajen rage fitar da hayakin Carbon mai dumama yanayi. Na biyu, kasar Sin tana da fifiko wajen masana’antun samar da wutar lantarki ta makamashin rana, da karfin iska, da kuma motoci masu amfani da lantarki, wadanda kuma ke samar da alfanu ga karin kasashe ta hadin gwiwarsu da kasar Sin bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”. Na uku kuma, kirkire-kirkiren da kasar Sin ta yi wajen bunkasa tattalin arziki mai alaka da kiyaye muhalli sun samar da misali ga aikin kiyaye muhalli a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

A cikin ‘yan shekarun baya, hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ta fannin kiyaye muhalli ya janyo hankalin duniya sosai. Kasar Sin ta aiwatar da daruruwan ayyuka masu alaka da tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba a Afirka, kuma ta hanyar musayar fasahohi da shirye-shirye da kuma samar da tallafin kudi, kasar Sin ta yi ta inganta hadin gwiwarta da kasashen Afirka ta fannin samar da makamashi masu tsabta. Kamar yadda Brains Muchemwa, masanin ilmin tattalin arzikin kasar Zimbabwe ya ce, kasashen Afirka sun amfana sosai da masana’antun samar da makamashi masu tsabta da ke saurin bunkasa a kasar Sin.

A yayin da take kokarin zamanantar da kanta, kasar Sin tana son raba fasahohinta masu alaka da samun ci gaban kasa ba tare da gurbata muhalli ba, haka kuma tana son aiwatar da wasu ayyuka bisa hadin gwiwa da kasashen Afirka, a kokarin samun ci gaban tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, da tabbatar da zamanantarwa gami da kyakkyawan muhalli a lokaci guda.

 

Beijing
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Beijing
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika

Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika

LABARAI MASU NASABA

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.