• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Dan Nijeriya Ya Harbe Matarsa Da Kakarsa, Ya Kuma Kashe Kansa A Amurka

by Muhammad
3 years ago
in Al'ajabi
0
Wani Dan Nijeriya Ya Harbe Matarsa Da Kakarsa, Ya Kuma Kashe Kansa A Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani dan Nijeriya mai suna, Obinna Igbokwe, a ranar Alhamis ya harbe matarsa ​​Tangela da kakarsa kafin ya kashe kansa a jihar Texas ta Amurka.

Ko da yake matar ta samu munanan raunuka kuma tana kwance a asibiti, kakar ta rasu sakamakon raunin da ta samu.

  • Matar Da Ake Yi Wa Allurar Tazarar Haihuwa Ta Haifi ‘Yan Hudu Rigis
  • Fashewar Tukunyar Gas Ta Raunata Mutan 20 Da Kona Wasu Shaguna A Kano

A cewar wani rahoto na kasar, Igbokwe ya bar gida ne tare da dansa dan watanni uku, bayan ya harbe matan biyu a ka a ranar Laraba.

Yayin da suka gudu, Igbokwe ya ajiye yaron a kujerar mota a wani otal.

Lokacin da aka sanar da ‘yan sanda cewar yana yankin, wanda ake zargin ya harbe kansa ya mutu sakamakon raunin da ya samu.

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Wata sanarwa da ofishin Sheriff ta fitar a ranar Alhamis ta ce, “A ranar 2 ga watan Yuni, 2022, da misalin karfe 12:00 na safe, jami’an tsaro na ofishin Sheriff na Montgomery sun tuntubi jami’an ‘yan sanda na Corsicana kuma suka ba da shawarar cewa Mansa Igbokwe ke kula da su.

“A cewar hukumar ‘yan sanda ta Corsicana, wani namiji ya ajiye yaron a kujerar mota a wani otal da ke yankin ya ce zai dawo nan da nan, amma bai dawo ba.

“Tunda namijin bai dawo ba, sai aka tuntubi hukumar ‘yan sanda ta Corsicana, inda suka samu labarin ya bar mutumin a cikin wata farar motar fasinja, wadda suka yi imanin Igbokwe ne.

“An aika da ƙarin bayanai ga jami’an tsaro na yankin Ellis da Navarro suna sanar da su cewa Igbokwe na yankin.

“Da misalin karfe 1:05 na dare jami’an hukumar ‘yan sanda ta Ennis sun gano wata farar mota kirar Honda Igbokwe tana tuki kuma suka yi yunkurin tsayar da motar.

“Bayan sun bibiyi motar kirar Honda sai ta tsaya a wani wurin ajiye motoci inda jami’ansu suka lura kuma suka ji karar harbin bindiga daya fito daga cikin motar Honda.

“Jami’an tsaro sun fara daukar matakan ceton rai tare da kiran jami’an lafiya, amma saboda tsananin raunin da Igbokwe ya samu abun ya ci tura, an garzaya da shi wani asibiti mai suna Dallas da misalin karfe 5:20 na safe.

“Mansa Igbokwe yana cikin koshin lafiya kuma bai samu matsala ba kuma ya sake haduwa da iyalinsa. Zuciyarmu tana tare da dangin da wannan mummunan laifi ya shafa kuma muna aiki tare da wadanda abin ya shafa don ganin sun sami tallafi da taimako.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amurka
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Fitar Da Sabbin Ka’idojin Zaben 2023

Next Post

NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

1 month ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

2 months ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

2 months ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

3 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

3 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

3 months ago
Next Post
NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta

NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.