• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Akida Ta Sa Sinawa Likitoci Shiga Cikin Hamadar Sahara

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wannan Akida Ta Sa Sinawa Likitoci Shiga Cikin Hamadar Sahara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Errachidia wani gari ne dake gabashin kasar Morocco, wanda ya kasance cikin hamadar Sahara. Mazauna garin kowanensu ya san “likitocin kasar Sin”, domin wata tawagar likitocin kasar Sin ta riga ta kwashe shekaru 38 tana samar da hidimomi a can. Ana ma iya cewa kusan rabin yaran wurin likitocin Sin ne suka karbi haihuwar su, kana a kan samu iyalin da mambobinsa na zuriyoyi 3 suka taba samun taimako daga likitocin.

Kasancewar garin Errachidia wani kebabben wurin dake cikin hamada, ya sa shi rashin kayayyaki da abubuwa iri-iri, musamman ma likitoci. Saboda haka, likitoci 10 na wannan tawagar agajin aikin jinya ta Sin su kan gudanar da ayyukan tiyata fiye da 2000 a duk shekara. Wani lokaci ma, wani likita daya dake cikinsu na bukatar yin tiyata kan majiyyata 8 daya bayan daya a dare daya.

  • Firaministan Kambodiya: Takunkuman Da Ake Sanyawa Babu Tsayawa Na Haifar Da Tashe-Tashen Hankali A Duniya

Don haka su kan yi fama da rashin barci da gajiyar aiki. Jiang Quanming, mai shekaru 56 da haihuwa, shugaba ne na wannan tawagar likitocin Sin, wanda ya taba fita hayyacinsa yayin da yake aiki sakamakon matukar gajiya. Amma duk da haka, ya tsawaita wa’adin aikinsa a wurin bisa son ransa. A cewarsa, makiyayan wurin su kan yi kokarin jure ciwon jiki yayin da suke rashin lafiya, sakamakon tsananin talaucin da suke fama da shi, abin da ya sa su cikin wani yanayi mai hadari bayan da aka kai su asibiti a karshe. Saboda haka, duk wani aikin tiyata da shi da abokan aikinsa suka yi, zai ceci ran mutum daya.

Maganar Jiang ta nuna yadda likitan yake da kishi da kokarin sadaukarwa, sai dai ba zai samu damar cimma burinsa na taimakawa mutanen garin Errachidia, in ba domin goyon bayan da gwamnatin kasar Sin ta nuna masa, da kudin da ta zuba ba. Hakika tura tawagogin agajin aikin likitanci zuwa ketare wani muhimmin bangare ne na aikin kasar Sin, na tallafawa sauran kasashen da suke da bukata.

A shekarar 1963, kasar Sin ta tura tawagarta ta farko ta ba da agajin aikin jinya zuwa kasar Aljeriya. Daga baya, cikin shekaru 60 da suka wuce, kasar Sin ta tura likitoci dubu 30 zuwa kasashe da yankuna 76. Bayan da annobar Ebola ta barke a yammacin Afirka, kasar Sin ta tura likitoci fiye da 1200 zuwa wuraren da aka fi jin radadin annobar don ba da taimako. Kana a lokacin da ake samun bazuwar cutar COVID-19 a duniya, tawagogin likitocin Sin 46 dake kasashen Afirka daban daban, sun samar da gudunmowa a kokarin dakile annobar a wuraren da suke. Sa’an nan, tawagogin likitocin Sin sun ba da kyautar dimbin magunguna da sauran kayayyakin aikin jinya ga wasu asibitocin kasashe masu tasowa, gami da taimaka musu horar da masu aikin likitanci.

Labarai Masu Nasaba

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

Ko me ya sa kasar Sin ke son ba da taimako ga sauran kasashe a fannin aikin likitanci? Dalilin shi ne aikin ya dace da al’adun Sinawa na daukaka zaman lafiya da darajanta rayukan mutane. Wannan al’adu sun sa kasar Sin son tabbatar da kwanciyar hankali maimakon ta da rikici, da kai dauki ga wadanda ke da bukata, maimakon nade hannu a yi kallo a gefe. Saboda haka, a lokacin da ake bukatar likitoci da magunguna a wasu kasashe masu tasowa, kasar Sin ta kan tura likitoci da samar da tallafi ba tare da jinkiri ba. Kana bayan da aka samu barkewar rikici a wasu kasashe, sojojin Sin su kan aiwatar da aikin kiyaye zaman lafiya a can, bisa izinin da Majilissar Dinkin Duniya (UN) ta ba su. Kana duk lokacin da wani iftila’i ya abku, kasar Sin ta kan tura tawagogin ceto, da aikewa da kayayyakin da ake bukata nan take, ba tare da wani jinkiri ba ko kadan.

Ban da haka kuma, wani babban dalilin da ya sa kasar Sin ke kokarin tallafawa sauran kasashe a fannin aikin likitanci, shi ne akidarta ta “kafa wata al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya”. A cikin gidan kasar, an samu kawar da talauci, da kokarin neman wadatar da dukkan al’ummun kasar, lamarin da ya sa ake samun zaman jituwar al’umma, da ci gaban tattalin arziki mai dorewa. Saboda haka, kasar Sin na ganin cewa, kamata ya yi, a yi kokarin tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban na bai daya, inda za a dinga rage gibin dake tsakanin kasashe, da na zaman rayuwar al’ummu daban daban, ta yadda za a iya daidaita matsalolin da dan Adam ke fuskantar, da kafa wata duniya mai jituwa.

A lokacin da ka ga yadda likitoci Sinawa suke kokarin haye wahalhalun da suke ba da taimako ga jama’a a cikin hamadar Sahara, to, za ka fahimci cewa, Sinawa na kokarin aiwatar da akidarsu ta kafa wata al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, kana burinsu na samun wata duniya mai kyau zai cika. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI-DUMI: ‘Yan Bindiga Sun Kashe DPO Da Wasu Mutum 4 A Neja

Next Post

Ina Yin Fim Ne Ta Yadda Ko Da Surikai Suka Kalla Ba Za Su Kunyata Ba —Mai-Kwashewa

Related

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
Daga Birnin Sin

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

16 hours ago
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

17 hours ago
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Daga Birnin Sin

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

19 hours ago
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

19 hours ago
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
Daga Birnin Sin

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

20 hours ago
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

21 hours ago
Next Post
Ina Yin Fim Ne Ta Yadda Ko Da Surikai Suka Kalla Ba Za Su Kunyata Ba —Mai-Kwashewa

Ina Yin Fim Ne Ta Yadda Ko Da Surikai Suka Kalla Ba Za Su Kunyata Ba —Mai-Kwashewa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.