• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Taro Ya Nuna Cewa Afirka Na Da Wani Sahihin Aboki

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Wannan Taro Ya Nuna Cewa Afirka Na Da Wani Sahihin Aboki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ta yaya za a gane ko wani mutum yana da gaskiya? Ta hanyar gaya masa bukatarka, sa’an nan a duba yadda zai mayar maka da martani. Zai nuna yanayin ko-in-kula, ko kuma zai yi kokarin ba ka amsa mai gamsarwa.

 

A ranar 12 ga wata, kasar Saliyo, bisa matsayinta na kasar dake shugabantar kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya na karba karba, ta shirya wani taron muhawara, don tattauna batun kara kujerun kasashen Afirka cikin kwamitin sulhun.

  • Xi Ya Yabawa ‘Yan Wasan Olympics Na Sin Da Suka Samarwa Kasar Daukaka 
  • Peng Liyuan Ta Gana Da Uwar Gidan Shugaban Vietnam

Yayin da yake jawabi, shugaban kasar Saliyo Julius Bio ya ce, har yanzu babu wata kujerar din-din-din ta nahiyar Afirka a kwamitin, kana babu isassun kujeru wadanda ba na din-din-din ba mallakar kasashen Afirka, lamarin da a cewarsa ya nuna rashin adalci irin na tarihi.

 

Labarai Masu Nasaba

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

A nata bangare, Sithembile Mbete, wata masaniyar ilimin siyasa ta kasar Afirka ta Kudu, ita ma ta ba da jawabi wajen taron, inda ya yi karin tsokaci kan batun rashin adalci da kasashen Afirka ke fuskanta. A cewarta, asalin rashin adalcin shi ne cinikin bayi da kasashen yamma suka kwashe shekaru 400 suna yi, da yadda kasashen Turai da kasar Amurka suka kasa nahiyar Afirka zuwa yankunan mulkin mallaka daban daban, a wani taron da suka gudanar a birnin Berlin na kasar Jamus a shekarar 1884.

 

Abin lura shi ne, dangane da jawaban da wakilan kasashen Afirka suka yi, wadanda suka nuna rashin jin dadinsu, game da rashin adalci da aka yi musu, kasar Amurka ta nuna yanayin ko-in-kula, ko da yake ta taba halarta da cin moriyar cinikin bayi, gami da kasancewarsa a teburin tattaunawar taron Berlin na shekarar 1884. Yayin da wakiliyar kasar Amurka a MDD Linda Thomas-Greenfield ke ba da jawabi, ta ambaci maganar da shugaban kasarta Joseph Biden ya yi, ta “nuna goyon baya ga Afirka, da Latin Amurka, da kasashen Caribbeans kan batun neman kujerun din-din-din a kwamitin sulhun MDD” kadai, ba tare da tabo maganar rashin adalci da Afirka ke fuskanta ba, balle ma tuba kan laifukan da kasar Amurka ta taba aikatawa.

 

A dai wajen wannan taro, dangane da bukatar kasashen Afirka, ta yaya kasar Sin ta mayar da martani? A cikin jawabinsa, wakilin Sin a MDD Fu Cong ya nuna goyon baya ga nahiyar Afirka, inda ya yi Allah wadai da cin zarafin al’ummun nahiyar Afirka da kasashen yamma suka yi a tarihi, da bayyana matakan da suka dauka a matsayin asalin rashin adalci dake damun kasashen Afirka. Kana ya ce har yanzu wannan yanayi na rashin adalci na ci gaba, ganin yadda wasu kasashen yamma ke tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, da neman cin zarafi da sarrafa su.

 

Daga baya, Fu Cong ya ba da shawara kan matakan da ya kamata a dauka, don daidaita yanayin rashin adalci dake damun kasahen Afirka. A cewarsa, da farko, ya kamata kasashen yamma su daina tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, da mayar wa jama’ar kasashen Afirka cikakken ikon kula da kai, da tabbatar da makomar kai.

 

Na biyu, a taimaki kasashen Afirka a kokarinsu na samun ci gaba mai dorewa, da raya masana’antu, da zamanantarwa.

 

Na uku, a tabbatar da samun dimbin bangarori masu fada a ji a duniya, da nuna cikakken goyon baya ga kasashen Afirka, kan bukatarsu ta yin gyare-gyare kan tsarin kwamitin sulhun MDD.

 

Kana na hudu, a gyara tsarin hada-hadar kudi ta duniya, don samar da karin tallafi ga kasashen Afirka, da kawo karshen matakin wasu kasashe na yin amfani da manufar kudin su wajen kwace dukiyoyin da jama’ar kasashen Afirka suka tattara.

 

A zahiri kasar Sin tana goyon bayan kasashen Afirka, har ma ta samar da shawarwari masu amfani. Idan ka san manufofin kasar Sin, to, za ka gane duk wadannan shawarwari na cikin manufofin kasar na dogon lokaci.

 

Idan mun kalli taron kwamitin sulhun MDD da ya gudana a matsayin wata jarrabawa kan cewar “ko ana nuna gaskiya da sahihanci ga kasashen Afirka”, to, na san kasar Sin ta ci jarrabawar. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gana Da Shugabannin Majalisun Dokokin Kasashen Duniya

Next Post

Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

Related

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

4 days ago
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

5 days ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

7 days ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

1 week ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

2 weeks ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 weeks ago
Next Post

Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

October 4, 2025
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.