ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Taro Ya Nuna Cewa Afirka Na Da Wani Sahihin Aboki

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Afirka

Ta yaya za a gane ko wani mutum yana da gaskiya? Ta hanyar gaya masa bukatarka, sa’an nan a duba yadda zai mayar maka da martani. Zai nuna yanayin ko-in-kula, ko kuma zai yi kokarin ba ka amsa mai gamsarwa.

 

A ranar 12 ga wata, kasar Saliyo, bisa matsayinta na kasar dake shugabantar kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya na karba karba, ta shirya wani taron muhawara, don tattauna batun kara kujerun kasashen Afirka cikin kwamitin sulhun.

ADVERTISEMENT
  • Xi Ya Yabawa ‘Yan Wasan Olympics Na Sin Da Suka Samarwa Kasar Daukaka 
  • Peng Liyuan Ta Gana Da Uwar Gidan Shugaban Vietnam

Yayin da yake jawabi, shugaban kasar Saliyo Julius Bio ya ce, har yanzu babu wata kujerar din-din-din ta nahiyar Afirka a kwamitin, kana babu isassun kujeru wadanda ba na din-din-din ba mallakar kasashen Afirka, lamarin da a cewarsa ya nuna rashin adalci irin na tarihi.

 

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

A nata bangare, Sithembile Mbete, wata masaniyar ilimin siyasa ta kasar Afirka ta Kudu, ita ma ta ba da jawabi wajen taron, inda ya yi karin tsokaci kan batun rashin adalci da kasashen Afirka ke fuskanta. A cewarta, asalin rashin adalcin shi ne cinikin bayi da kasashen yamma suka kwashe shekaru 400 suna yi, da yadda kasashen Turai da kasar Amurka suka kasa nahiyar Afirka zuwa yankunan mulkin mallaka daban daban, a wani taron da suka gudanar a birnin Berlin na kasar Jamus a shekarar 1884.

 

Abin lura shi ne, dangane da jawaban da wakilan kasashen Afirka suka yi, wadanda suka nuna rashin jin dadinsu, game da rashin adalci da aka yi musu, kasar Amurka ta nuna yanayin ko-in-kula, ko da yake ta taba halarta da cin moriyar cinikin bayi, gami da kasancewarsa a teburin tattaunawar taron Berlin na shekarar 1884. Yayin da wakiliyar kasar Amurka a MDD Linda Thomas-Greenfield ke ba da jawabi, ta ambaci maganar da shugaban kasarta Joseph Biden ya yi, ta “nuna goyon baya ga Afirka, da Latin Amurka, da kasashen Caribbeans kan batun neman kujerun din-din-din a kwamitin sulhun MDD” kadai, ba tare da tabo maganar rashin adalci da Afirka ke fuskanta ba, balle ma tuba kan laifukan da kasar Amurka ta taba aikatawa.

 

A dai wajen wannan taro, dangane da bukatar kasashen Afirka, ta yaya kasar Sin ta mayar da martani? A cikin jawabinsa, wakilin Sin a MDD Fu Cong ya nuna goyon baya ga nahiyar Afirka, inda ya yi Allah wadai da cin zarafin al’ummun nahiyar Afirka da kasashen yamma suka yi a tarihi, da bayyana matakan da suka dauka a matsayin asalin rashin adalci dake damun kasashen Afirka. Kana ya ce har yanzu wannan yanayi na rashin adalci na ci gaba, ganin yadda wasu kasashen yamma ke tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, da neman cin zarafi da sarrafa su.

 

Daga baya, Fu Cong ya ba da shawara kan matakan da ya kamata a dauka, don daidaita yanayin rashin adalci dake damun kasahen Afirka. A cewarsa, da farko, ya kamata kasashen yamma su daina tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, da mayar wa jama’ar kasashen Afirka cikakken ikon kula da kai, da tabbatar da makomar kai.

 

Na biyu, a taimaki kasashen Afirka a kokarinsu na samun ci gaba mai dorewa, da raya masana’antu, da zamanantarwa.

 

Na uku, a tabbatar da samun dimbin bangarori masu fada a ji a duniya, da nuna cikakken goyon baya ga kasashen Afirka, kan bukatarsu ta yin gyare-gyare kan tsarin kwamitin sulhun MDD.

 

Kana na hudu, a gyara tsarin hada-hadar kudi ta duniya, don samar da karin tallafi ga kasashen Afirka, da kawo karshen matakin wasu kasashe na yin amfani da manufar kudin su wajen kwace dukiyoyin da jama’ar kasashen Afirka suka tattara.

 

A zahiri kasar Sin tana goyon bayan kasashen Afirka, har ma ta samar da shawarwari masu amfani. Idan ka san manufofin kasar Sin, to, za ka gane duk wadannan shawarwari na cikin manufofin kasar na dogon lokaci.

 

Idan mun kalli taron kwamitin sulhun MDD da ya gudana a matsayin wata jarrabawa kan cewar “ko ana nuna gaskiya da sahihanci ga kasashen Afirka”, to, na san kasar Sin ta ci jarrabawar. (Bello Wang)

Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post

Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.