• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan masharhanta da dama na ta tsokaci game da yawaitar hare-haren bindiga, na kan mai tsautsayi da ake samu a Amurka, lamarin da akasarin masu fashin baki ke alakantawa da mummunar akidar nan ta wariyar launin fata mai tsohon tarihi a kasar, da son cin zali na turawa masu rajin fifita fararen fata, tare da yawaitar mallaka, da amfani da makamai tsakanin fararen hular kasar.

Alkaluma sun nuna cewa, daga farkon shekarar nan ta 2023 zuwa yanzu kadai, an samu harbe-harben kan-mai-uwa da wabi har 146, ciki har da wanda aka hallaka wasu ’yan makarantar firamare 3, da wasu manya 3 a birnin Nashville, da wanda ya auku a jihar Kentucky a ranar Litinin, wanda ya sabbaba rasuwar mutane 4.

  • Xi Jinping: Turbar Zamantarwa Ta Kasar Sin Tana Da Manufa, Tsare-tsare Da Dabaru

A fili take cewa, Amurkawa da shekarun haihuwarsu ya kai 18, na da ikon saye ko rike bindiga, ciki kuwa har da manyan bindigogi masu hadarin gaske, wanda hakan ke kara ta’azzara yanayin tsaron fararen hula. Sannu a hankali, tashe-tashen hankula masu nasaba da harbin bindiga sun samu gindin zama a Amurka. Masana da yawa na cewa, baya ga batun saukin mallakar bindigogi, akwai kuma matsalar fatara, da gallazawa da wasu sassan al’ummun kasar ke fuskanta, wadanda su ma ke kara rura wutar wannan matsala.

Kisan bakar fatan nan mai suna George Floyd, da wasu ’yan sanda fararen fata suka yi a birnin Minneapolis a shekarar 2020, shaida ce da ta kara fayyace yadda wasu sassan al’ummar Amurka ke fuskantar nuna wariya da kyama. Alkaluma sun tabbatar da cewa, mutane da ba asalin fafaren fata ba ne, sun fi fuskantar muzgunawa a Amurka. Kuma wani karin abun takaici ma shi ne yadda wasu ’yan siyasar kasar ke amfani da kalamai na tunzura akidar nuna wariya, a matsayin dabar siyasa ta jan ra’ayin magoya baya.

A daya hannun kuma, mun san cewa cinikin makamai wani ginshiki ne na bunkasar tattalin arzikin Amurka, don haka mamallaka kamfanonin kera makamai, da masu nema musu goyon baya wajen ’yan siyasa, suka zamo kadangaren bakin tulu, wajen dakile matsalar raba fararen hular kasar da makamai masu hadari.

Labarai Masu Nasaba

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Abun tambaya a nan shi ne, idan aka gaza kare rayukan al’umma, shin ina sauran wani batun kare hakkin bil adama?

Maimaituwar hare-haren bindiga kan fararen hula a sassan Amurka, na nuni ga yadda gwamnatin kasar ta kasa fahimtar cikakkiyar ma’anar ’yancin bil adama, wanda ya hada da kare rayukan yara kanana, da matasa daga farmakin ’yan bindiga dadi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Onoja Da Asuku Sun Janye Daga Takarar Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Ya Zabi Ododo A Matsayin Magajinsa

Next Post

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 23

Related

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

13 hours ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

14 hours ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

15 hours ago
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
Daga Birnin Sin

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

16 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

1 day ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

1 day ago
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 23

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 23

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.