ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

by CMG Hausa
3 years ago
Makamai

A baya bayan nan masharhanta da dama na ta tsokaci game da yawaitar hare-haren bindiga, na kan mai tsautsayi da ake samu a Amurka, lamarin da akasarin masu fashin baki ke alakantawa da mummunar akidar nan ta wariyar launin fata mai tsohon tarihi a kasar, da son cin zali na turawa masu rajin fifita fararen fata, tare da yawaitar mallaka, da amfani da makamai tsakanin fararen hular kasar.

Alkaluma sun nuna cewa, daga farkon shekarar nan ta 2023 zuwa yanzu kadai, an samu harbe-harben kan-mai-uwa da wabi har 146, ciki har da wanda aka hallaka wasu ’yan makarantar firamare 3, da wasu manya 3 a birnin Nashville, da wanda ya auku a jihar Kentucky a ranar Litinin, wanda ya sabbaba rasuwar mutane 4.

  • Xi Jinping: Turbar Zamantarwa Ta Kasar Sin Tana Da Manufa, Tsare-tsare Da Dabaru

A fili take cewa, Amurkawa da shekarun haihuwarsu ya kai 18, na da ikon saye ko rike bindiga, ciki kuwa har da manyan bindigogi masu hadarin gaske, wanda hakan ke kara ta’azzara yanayin tsaron fararen hula. Sannu a hankali, tashe-tashen hankula masu nasaba da harbin bindiga sun samu gindin zama a Amurka. Masana da yawa na cewa, baya ga batun saukin mallakar bindigogi, akwai kuma matsalar fatara, da gallazawa da wasu sassan al’ummun kasar ke fuskanta, wadanda su ma ke kara rura wutar wannan matsala.

ADVERTISEMENT

Kisan bakar fatan nan mai suna George Floyd, da wasu ’yan sanda fararen fata suka yi a birnin Minneapolis a shekarar 2020, shaida ce da ta kara fayyace yadda wasu sassan al’ummar Amurka ke fuskantar nuna wariya da kyama. Alkaluma sun tabbatar da cewa, mutane da ba asalin fafaren fata ba ne, sun fi fuskantar muzgunawa a Amurka. Kuma wani karin abun takaici ma shi ne yadda wasu ’yan siyasar kasar ke amfani da kalamai na tunzura akidar nuna wariya, a matsayin dabar siyasa ta jan ra’ayin magoya baya.

A daya hannun kuma, mun san cewa cinikin makamai wani ginshiki ne na bunkasar tattalin arzikin Amurka, don haka mamallaka kamfanonin kera makamai, da masu nema musu goyon baya wajen ’yan siyasa, suka zamo kadangaren bakin tulu, wajen dakile matsalar raba fararen hular kasar da makamai masu hadari.

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Abun tambaya a nan shi ne, idan aka gaza kare rayukan al’umma, shin ina sauran wani batun kare hakkin bil adama?

Maimaituwar hare-haren bindiga kan fararen hula a sassan Amurka, na nuni ga yadda gwamnatin kasar ta kasa fahimtar cikakkiyar ma’anar ’yancin bil adama, wanda ya hada da kare rayukan yara kanana, da matasa daga farmakin ’yan bindiga dadi.

Makamai
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 23

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 23

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.