• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da Ghana ke shirin karbar bakuncin gasar wasannin Afirka da aka jinkirta a shekarar 2023, masu shirya wasannin cikin gida sun kwara ruwan sanyi kan fargabar da ake yi, inda suka ce kasar ta shirya tsaf domin gudanar da gasar wasannin.

An dage wasannin da aka shirya gudanarwa a watan Agustan shekarar 2023 saboda rashin daidaito da aka samu kan hakkin tallace-tallace wanda ya kawo tsaikon kammala filayen gudanar da wasannin, tare da rashin jituwa tsakanin kungiyoyin da suka hada da masu shirya gasar, da ta tarayyar Afrika (AU), da kungiyar kwamitocin Olympics na Afirka (Anoca) da kuma kungiyar hukumomin wasannin Afrika.

  • Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri
  • Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Duka kungiyoyi uku na taka muhimmiyar rawa wajen shirya gasar wanda a yanzu aka shirya aka fara gasar a Accra a ranar 8 ga Maris, a kuma kammala ranar 23 ga watan na Maris.

Mai magana da yawun kwamitin shirya wasannin na Afirka (LOC), Dan Kwaku Yeboah, ya bayyana cewa wannan wata dama ce ta musamman a gare su, su kasar Ghana domin yin abin a zo a gani.

Ya ce “An fara gudanar da wasannin Afirka ne tun a shekarar 1965, kuma in ban da Nijeriya babu wata kasa ta yammacin Afirka da ta samu damar karbar bakuncin gasar gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

Yeboah ya kara da cewa suna shirye daga kowane bangare, daga ababen more rayuwa da masauki da sufuri da kafofin yada labarai kuma kowanne tsari yana kan hanya sai dai an dan jinkirta aikin tantancewa.

Daya daga cikin tawagogin da tafiyar hawainiyar tantancewar ta shafa ita ce kasar Kamaru, wanda ‘yan wasa da jami’anta da na kafofin yada labarai suka fuskanci karancin lokaci wurin tabbatar da matsayinsu a Ghana.

Amma Sakataren Kwamitin Wasannin Olympic na Kamaru, Dabid Ojong ya ce da farko jami’insu ya samu ‘yan matsaloli wajen fahimtar yadda ake aiki da dandalin tantancewar, amma yayin wani zama da ya yi da LOC ta Intanet, an ba shi haske kan yadda dandalin ke aiki.

Yayin da aka fara gasar a hukumance, an kuma nuna damuwa kan yadda Ghana za ta iya gudanar da wasannin duba da irin halin tattalin arzikin da kasar take ciki.

Wani mai sharhi kan harkokin wasanni na Afirka ta Kudu, Duane Dell’Oca ya ce, har wani bangaren filin motsa jiki ya fara lalacewa inda ya fara nuna alamun tsagewa, kuma makonni kadan da suka gabata aka shimfida shi.

Matsalar rashin manyan taurarin afirka a gasar

An tabbatar da wasanni 29 a gasar wasannin ta Afrika, da wasannin guje-guje da tsalle-tsalle, da wasan kwallon badminton, da tseren keke, da ninkaya, da wasan tennis, da kuma kokawa, domin zama na masu neman cancantar shiga gasar Olympics a Birnin Paris 2024.

Duk da haka, lokacin gudanar da wasannin na nufin da yawa daga cikin fitattun masu fafatawa a Afirka ba za su halarta ba, wannan babbar matsala ce ga wadanda ke tallata gasar, a cewar Dell’Oca. Dell’Oca ya ce ba su samu damar tallata hotunan manyan ‘yan wasan Afirka da yawa ba saboda an samu rudani sosai kan wadanda za su fafata a gasar kuma hakan babbar barazana ce.

Tsohuwar ‘yar wasan Bolley Ball ta Kenya Jannet Wanja, wadda a yanzu ita ce mai horar da ‘yan wasan kasar, ita ma ta koka kan rashin samun halarcin manyan taurarin ‘yan wasa.

Ta ce a lokuta da yawa wasannin sun samu koma baya saboda rashin manyan ‘yan wasa da taurari da za su iya karawa gasar daraja, kuma sau da yawa ana hana manyan ‘yan wasa zuwa wanda kuma hakan ba ya taimakawa kuma Afirka ma tana da mahimmanci.

Ta ci gaba da cewa duk da kalubalen da ake fuskanta a gasar, tana da kwarin gwiwar samun nasarar gudanar da gasar wasannin Afirka a Ghana kuma yawancin kasashe har yanzu suna fama da tasirin cutar Korona, sannan matakan shirye-shiryensu sun yi kasa da abin da ake bukata, amma har yanzu tana fatan samun nasarar gasar.

Ojong ya ce, duk fargabar da ake yi game da filayen wasa da kayan aiki, dukkanin kungiyoyi za su fuskanci batutuwa iri daya.

“Idan LOC da kungiyoyin kasa da kasa sun tabbatar da cewa filayen sun dace da wasa, dole ne tawagogi su yi wasa a filayen yadda su ke.” in ji shi.

“Kowa zai yi wasa a wuri guda, kowa zai fukanci matsaloli iri daya, kuma hakan zai zama wani bangare na wasan.”

Ghana tana matukar farin ciki

Bayan murnar gasar cin kofin nahiyar Afirka da aka kammala kwanan nan a kasar Ibory Coast, Yeboah ya ce ya kamata ‘yan kallo da ‘yan wasa da jami’ai su sa rai cewa za a gudanar da gasar da ba za a manta da ita ba a nahiyar Afirka.

Ya kara da cewa ya kamata Afirka ta yi tsammaci irin karamci da al’adun Ghana da aka saba gani – su yi tsammanin za a gudanar da bikin bude gasa mai matukar kayatarwa kuma ya kamata su kyautata zaton ganin wasanni masu kayatarwa da kuma kyakkyawan yanayi a tattare da gasar saboda ‘yan Ghana na cikin matukar farin ciki.

Ana sa ran manyan wakilan kungiyar AU da shugabannin kasashe daban-daban da kuma ‘yan wasa sama da 5,000 da jami’ai daga sassan nahiyar su halarci gasar wanda za a shafe tsawon mako biyu ana gudanarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri

Next Post

Shugaban Jamhuriyar Congo: Ra’ayin Sabon Mulkin Mallaka Ba Shi Da Tushe

Related

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City
Wasanni

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

6 hours ago
Boniface
Wasanni

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

2 days ago
Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
Wasanni

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

3 days ago
Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0
Wasanni

Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0

5 days ago
Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

6 days ago
Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
Wasanni

Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?

6 days ago
Next Post
Shugaban Jamhuriyar Congo: Ra’ayin Sabon Mulkin Mallaka Ba Shi Da Tushe

Shugaban Jamhuriyar Congo: Ra’ayin Sabon Mulkin Mallaka Ba Shi Da Tushe

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.