• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasoso Da Fasa Rumbunan Hatsi Ba Za Su Magance Yunwa Ba – Farfesa Sanda

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NEMA Ta Musanta Mallakar Wani Rumbun Ajiyar Abinci Da Aka Wawashe A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shehin Malami kuma babban masani a bangaren tattalin arziki (Economy), Farfesa Ahmad Sanda, da ke aiki a jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sokoto a tsangayar koyar da nazarin tattalin arziki, ya shaida cewar, matsalar da matasa ke haifarwa ta zuwa rumbunan adana kayan abinci da fasawa domin kwashewa ko daka wasoso ga mo-tocin dakon kayan abinci ba za su shawo kan matsalolin matsin rayuwa da ake ciki ba illa ma kara jefa kasar cikin mayuwacin hali.

Ya shaida cewar, ana cikin mawuyacin halin da akwai bukatar gwamnatoci da masu ruwa da tsaki za su tashi tsaye domin jawo hankalin matasa da su kauce wa dabi’ar fasa wurare da sunan neman abinci.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi

A cewarsa: “Wannan alama ce ta kamarin yunwa da tsadar rayuwa da ake ciki. Hanya mafi sauki ta shawo kan wannan matsalar shi ne gwamnati ta tabbatar duk wani kayan abinci da aka ware domin rabarwa a irin wannan yanayin ana kawowa a rabar ba wai a je a tara a ajiye a rumbu ba.

“Domin kwasan kayan abinci a kai rumbunan ajiye abinci mutane za su yi tunanin an ajiye ne domin a yi sama da fadi da su. In so samu ne daga inda aka kawo abinci domin rabarwa kawai a kai su ga jama’a kai tsaye a tabbatar an rabar. Kai tun kafin ma su iso a yi tsarin da suka dace suna zuwa a mika ga jama’a. A irin lokacin da talakawa ke matsin rayuwa gaskiya babu bukatar zuwa a ajiye abinci a boye.”

A cewarsa, akwai bukatar a tsaurara matakan tsaro domin fasa wuraren adana kayan abinci wata alama ce da ke nuni da cewa an tura mutane zuwa bango, don haka idan ba a dauki matakan tsaro ba, nan gaba sai an rasa wurin da za a ajiye wani abu da sunan abinci, “A daidai gabar daukan matakin tsaro gwamnati ta tabbatar tana raba wa jama’a abinci ba zuwa a boye ba.”

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

Dangane da masu daka wasoso kan kayan abinci a motocin dakon ‘yan kasuwa, bab-ban malamin ya ce, akwai fa babban matsala, yana mai cewa hakan ba zai yi komai ba illa kara jefa farashin kayayyaki domin ya yi tsada.

“Gaskiya wadannan matsalolin sun shafi wasu abubuwa da suka ma zarce sashin tat-talin arziki shi kadai. Domin babu wani bangare a bangaren tattalin arziki da ya bai wa jama’a damar daka wawa kan kayan mutane.

“Akwai bukatar masu ruwa da tsaki daga bangarori daban-daban su shigo cikin wan-nan matsalar, malamai su wayar da kai.

“Eh an sani idan mutane na cikin matsatsin rayuwa, mutane ba za su saurari wasu bayanan ba, amma ya kamata dukkanin masu ruwa da tsaki kowa ya fito ya tofa al-barkacin bakinsa da kuma yin abun da ya dace.

“Kuma yana da kyau a nusar da matasa illolin fasa kayan abincin mutane. Domin idan ana fasa kayayyakin mutane ba ma na gwamnati kadai ba har da na ‘yan kasuwa ka ga wannan ba cigaba zai kawo ba zai kara tabarbara tattalin arziki ne. domin hauhawar farashin kayayyaki da gwamnati ke kokarin ta ga ta shawo kansa abun zai ta’azzara.”

“Gwamnoni, shugabannin kananan malamai, limamai, fastoci, kungiyoyi, kowa da kowa da su fito su jawo hankalin matasa kan cewa daka wawa ga kayan jama’a ba shi ne mafita ga wannan matsalar ba, kuma ba zai haifar da da mai ido ba. Don a maima-kon a samu sassaucin kayayyaki to wasoso zai sa farashi ya kara yin sama ne.

“Domin dan kasuwa ya sayo kayansa ya yi asararsu ka ga ba zai koma ba hakan zai sanya a samu karancin kayayyakin da har farashi zai kara hauhawa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukunce-hukuncen Ganin Watan Ramadan

Next Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

3 minutes ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

52 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

2 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

7 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

15 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

LABARAI MASU NASABA

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.