• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasoso Da Fasa Rumbunan Hatsi Ba Za Su Magance Yunwa Ba – Farfesa Sanda

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
NEMA Ta Musanta Mallakar Wani Rumbun Ajiyar Abinci Da Aka Wawashe A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shehin Malami kuma babban masani a bangaren tattalin arziki (Economy), Farfesa Ahmad Sanda, da ke aiki a jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sokoto a tsangayar koyar da nazarin tattalin arziki, ya shaida cewar, matsalar da matasa ke haifarwa ta zuwa rumbunan adana kayan abinci da fasawa domin kwashewa ko daka wasoso ga mo-tocin dakon kayan abinci ba za su shawo kan matsalolin matsin rayuwa da ake ciki ba illa ma kara jefa kasar cikin mayuwacin hali.

Ya shaida cewar, ana cikin mawuyacin halin da akwai bukatar gwamnatoci da masu ruwa da tsaki za su tashi tsaye domin jawo hankalin matasa da su kauce wa dabi’ar fasa wurare da sunan neman abinci.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi

A cewarsa: “Wannan alama ce ta kamarin yunwa da tsadar rayuwa da ake ciki. Hanya mafi sauki ta shawo kan wannan matsalar shi ne gwamnati ta tabbatar duk wani kayan abinci da aka ware domin rabarwa a irin wannan yanayin ana kawowa a rabar ba wai a je a tara a ajiye a rumbu ba.

“Domin kwasan kayan abinci a kai rumbunan ajiye abinci mutane za su yi tunanin an ajiye ne domin a yi sama da fadi da su. In so samu ne daga inda aka kawo abinci domin rabarwa kawai a kai su ga jama’a kai tsaye a tabbatar an rabar. Kai tun kafin ma su iso a yi tsarin da suka dace suna zuwa a mika ga jama’a. A irin lokacin da talakawa ke matsin rayuwa gaskiya babu bukatar zuwa a ajiye abinci a boye.”

A cewarsa, akwai bukatar a tsaurara matakan tsaro domin fasa wuraren adana kayan abinci wata alama ce da ke nuni da cewa an tura mutane zuwa bango, don haka idan ba a dauki matakan tsaro ba, nan gaba sai an rasa wurin da za a ajiye wani abu da sunan abinci, “A daidai gabar daukan matakin tsaro gwamnati ta tabbatar tana raba wa jama’a abinci ba zuwa a boye ba.”

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

Dangane da masu daka wasoso kan kayan abinci a motocin dakon ‘yan kasuwa, bab-ban malamin ya ce, akwai fa babban matsala, yana mai cewa hakan ba zai yi komai ba illa kara jefa farashin kayayyaki domin ya yi tsada.

“Gaskiya wadannan matsalolin sun shafi wasu abubuwa da suka ma zarce sashin tat-talin arziki shi kadai. Domin babu wani bangare a bangaren tattalin arziki da ya bai wa jama’a damar daka wawa kan kayan mutane.

“Akwai bukatar masu ruwa da tsaki daga bangarori daban-daban su shigo cikin wan-nan matsalar, malamai su wayar da kai.

“Eh an sani idan mutane na cikin matsatsin rayuwa, mutane ba za su saurari wasu bayanan ba, amma ya kamata dukkanin masu ruwa da tsaki kowa ya fito ya tofa al-barkacin bakinsa da kuma yin abun da ya dace.

“Kuma yana da kyau a nusar da matasa illolin fasa kayan abincin mutane. Domin idan ana fasa kayayyakin mutane ba ma na gwamnati kadai ba har da na ‘yan kasuwa ka ga wannan ba cigaba zai kawo ba zai kara tabarbara tattalin arziki ne. domin hauhawar farashin kayayyaki da gwamnati ke kokarin ta ga ta shawo kansa abun zai ta’azzara.”

“Gwamnoni, shugabannin kananan malamai, limamai, fastoci, kungiyoyi, kowa da kowa da su fito su jawo hankalin matasa kan cewa daka wawa ga kayan jama’a ba shi ne mafita ga wannan matsalar ba, kuma ba zai haifar da da mai ido ba. Don a maima-kon a samu sassaucin kayayyaki to wasoso zai sa farashi ya kara yin sama ne.

“Domin dan kasuwa ya sayo kayansa ya yi asararsu ka ga ba zai koma ba hakan zai sanya a samu karancin kayayyakin da har farashi zai kara hauhawa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukunce-hukuncen Ganin Watan Ramadan

Next Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

Related

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

3 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

4 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

13 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

16 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

18 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

19 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.