• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ma’aikata Hudu Sun Damfari Karamin Bankin Kasuwanci Naira Miliyan 150 A Legas

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kotu Ta Wa Malamin Islamiyyan Da Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyade Daurin Rai Da Rai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’a ne aka gurfanar da wasu mutum hudu a gaban kotun Majistare ta Yaba bisa zargin damfarar bankin, Think Finance Microfinance Bank na Naira miliyan 150 a unguwar FESTAC Town a Jihar Legas.

Wadanda ake tuhumar sun hada da shugaban kamfanin na Risk Management, Ojimi Ayodeji, jami’in bayar da lamuni, Isaac Eddy, Joseph Setonji da Juwon Irinyemi, kuma an gurfanar da su a gaban Alkali Patrick Nwaka bisa laifuka uku na sata.

  • DSS Ta Fara Gayyatar Makusantan Dakataccen Shugaban EFCC, Bawa Bayan Binciken Ofishinsa Da Gidansa

Lauyan mai shigar da kara, Thomas Nurudeen, ya shaida wa kotun cewa wadanda ake tuhumar da kamfanin ke yi, an dora su ne da alhakin bayar da lamuni ga mutane don kasuwanci, amma sai suka hada baki suka yi amfani da sunaye na bogi wajen karbar kudi daga kamfanin har Naira miliyan 150 wanda suka raba tsakaninsu ba tare sun biya ba.

Wadanda ake tuhumar sun gabatar da daidaikun mutane tare da mika musu lambobin tantance banki da sunayen asusun ajiya da kuma hotunan fasfo wadanda ba na gaskiya ba ne don karbar kudin.

Nurudeen ya bayyana cewa wadanda ake tuhumar sun aikata laifin ne tsakanin shekarar 2019 zuwa Disamba 2022 a bankin Think Finance Microfinance Bank dake cikin garin FESTAC.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

A cewar Nurudeen laifuffukan sun ci karo da juna kuma ana hukunta su a karkashin sashe na 314, 325 (1) da 287 (a) (b) (e) na dokar laifuka ta Jihar Legas, 2015.

A wani bangare na tuhume-tuhumen ya karanto cewa, “Kai, Ojimi Ayodeji, Isaac Eddy, jami’in bayar da lamuni, Joseph Setonji, Juwon Irinyemi da sauran su a yanzu, tsakanin shekarar 2019 da Disamba 2022, a bankin Think Finance Microfinance Bank, garin FESTAC, Legas, a gundumar Legas, kun hada kai a tsakanin da juna don aikata laifukan damfara kuma ta haka ne kuka aikata laifin da zai sa hukunta ku a karkashin sashe na 325 (1) na dokar laifuka ta Jihar Legas, a shekarar 2015.

“Kai, Ojimi Ayodeji, shugaban kula da kadara, Isaac Eddy, jami’in bayar da lamuni, Joseph Setonji, Juwon Irinyemi, da sauran su a yanzu, tsakanin 2019 da Disamba 2022, a bankin Think Finance Microfinance Bank, FESTAC Town, Legas, a cikin Kotun Majistare ta Legas, sun yi zamba ta ware rancen Naira miliyan 150 ga wadanda kuka samar da lambarsu ta asusus da BBN da sunan asusun ajiya da hotunan fasfo wadanda ba na gaskiya ba, wakilcin da kuka san karya ne amma kuka aikata laifin, hakan ya sanya za a hukunta ku a karkashin sashe na 314 na dokar laifuka ta Legas, da aka gabatar a Jihar a 2015.”
Sai dai wadanda ake tuhumar sun ki amsa laifin da ake tuhumar su da shi.
Lauyan wadanda ake kara, Barista Ola, ya roki kotun da ta bayar da belinsu cikin mafi sassaucin ra’ayi.

Ba tare da adawa daga masu gabatar da kara ba, Nwaka ya amince da bayar da belinsu a kan kudi Naira miliyan 2 kowannen su tare da mutum hudu da za su tsaya musu.
Ya ce kowane wanda zai tsaya musu zai gabatar da takardar shaidar biyan haraji na shekaru uku da kotu za ta tantance, sannan ta dage sauraron karar har zuwa ranar 16 ga Agusta, 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasahar Sadarwa Ta Kwamfuta

Next Post

Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

3 days ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

3 days ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

June 3, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.