• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ma’aikata Hudu Sun Damfari Karamin Bankin Kasuwanci Naira Miliyan 150 A Legas

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kotu Ta Wa Malamin Islamiyyan Da Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyade Daurin Rai Da Rai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’a ne aka gurfanar da wasu mutum hudu a gaban kotun Majistare ta Yaba bisa zargin damfarar bankin, Think Finance Microfinance Bank na Naira miliyan 150 a unguwar FESTAC Town a Jihar Legas.

Wadanda ake tuhumar sun hada da shugaban kamfanin na Risk Management, Ojimi Ayodeji, jami’in bayar da lamuni, Isaac Eddy, Joseph Setonji da Juwon Irinyemi, kuma an gurfanar da su a gaban Alkali Patrick Nwaka bisa laifuka uku na sata.

  • DSS Ta Fara Gayyatar Makusantan Dakataccen Shugaban EFCC, Bawa Bayan Binciken Ofishinsa Da Gidansa

Lauyan mai shigar da kara, Thomas Nurudeen, ya shaida wa kotun cewa wadanda ake tuhumar da kamfanin ke yi, an dora su ne da alhakin bayar da lamuni ga mutane don kasuwanci, amma sai suka hada baki suka yi amfani da sunaye na bogi wajen karbar kudi daga kamfanin har Naira miliyan 150 wanda suka raba tsakaninsu ba tare sun biya ba.

Wadanda ake tuhumar sun gabatar da daidaikun mutane tare da mika musu lambobin tantance banki da sunayen asusun ajiya da kuma hotunan fasfo wadanda ba na gaskiya ba ne don karbar kudin.

Nurudeen ya bayyana cewa wadanda ake tuhumar sun aikata laifin ne tsakanin shekarar 2019 zuwa Disamba 2022 a bankin Think Finance Microfinance Bank dake cikin garin FESTAC.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

A cewar Nurudeen laifuffukan sun ci karo da juna kuma ana hukunta su a karkashin sashe na 314, 325 (1) da 287 (a) (b) (e) na dokar laifuka ta Jihar Legas, 2015.

A wani bangare na tuhume-tuhumen ya karanto cewa, “Kai, Ojimi Ayodeji, Isaac Eddy, jami’in bayar da lamuni, Joseph Setonji, Juwon Irinyemi da sauran su a yanzu, tsakanin shekarar 2019 da Disamba 2022, a bankin Think Finance Microfinance Bank, garin FESTAC, Legas, a gundumar Legas, kun hada kai a tsakanin da juna don aikata laifukan damfara kuma ta haka ne kuka aikata laifin da zai sa hukunta ku a karkashin sashe na 325 (1) na dokar laifuka ta Jihar Legas, a shekarar 2015.

“Kai, Ojimi Ayodeji, shugaban kula da kadara, Isaac Eddy, jami’in bayar da lamuni, Joseph Setonji, Juwon Irinyemi, da sauran su a yanzu, tsakanin 2019 da Disamba 2022, a bankin Think Finance Microfinance Bank, FESTAC Town, Legas, a cikin Kotun Majistare ta Legas, sun yi zamba ta ware rancen Naira miliyan 150 ga wadanda kuka samar da lambarsu ta asusus da BBN da sunan asusun ajiya da hotunan fasfo wadanda ba na gaskiya ba, wakilcin da kuka san karya ne amma kuka aikata laifin, hakan ya sanya za a hukunta ku a karkashin sashe na 314 na dokar laifuka ta Legas, da aka gabatar a Jihar a 2015.”
Sai dai wadanda ake tuhumar sun ki amsa laifin da ake tuhumar su da shi.
Lauyan wadanda ake kara, Barista Ola, ya roki kotun da ta bayar da belinsu cikin mafi sassaucin ra’ayi.

Ba tare da adawa daga masu gabatar da kara ba, Nwaka ya amince da bayar da belinsu a kan kudi Naira miliyan 2 kowannen su tare da mutum hudu da za su tsaya musu.
Ya ce kowane wanda zai tsaya musu zai gabatar da takardar shaidar biyan haraji na shekaru uku da kotu za ta tantance, sannan ta dage sauraron karar har zuwa ranar 16 ga Agusta, 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasahar Sadarwa Ta Kwamfuta

Next Post

Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

Related

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

2 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

2 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

3 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 months ago
Next Post
Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.