ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ma’aikata Hudu Sun Damfari Karamin Bankin Kasuwanci Naira Miliyan 150 A Legas

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Bankin kasuwanci

A ranar Juma’a ne aka gurfanar da wasu mutum hudu a gaban kotun Majistare ta Yaba bisa zargin damfarar bankin, Think Finance Microfinance Bank na Naira miliyan 150 a unguwar FESTAC Town a Jihar Legas.

Wadanda ake tuhumar sun hada da shugaban kamfanin na Risk Management, Ojimi Ayodeji, jami’in bayar da lamuni, Isaac Eddy, Joseph Setonji da Juwon Irinyemi, kuma an gurfanar da su a gaban Alkali Patrick Nwaka bisa laifuka uku na sata.

  • DSS Ta Fara Gayyatar Makusantan Dakataccen Shugaban EFCC, Bawa Bayan Binciken Ofishinsa Da Gidansa

Lauyan mai shigar da kara, Thomas Nurudeen, ya shaida wa kotun cewa wadanda ake tuhumar da kamfanin ke yi, an dora su ne da alhakin bayar da lamuni ga mutane don kasuwanci, amma sai suka hada baki suka yi amfani da sunaye na bogi wajen karbar kudi daga kamfanin har Naira miliyan 150 wanda suka raba tsakaninsu ba tare sun biya ba.

ADVERTISEMENT

Wadanda ake tuhumar sun gabatar da daidaikun mutane tare da mika musu lambobin tantance banki da sunayen asusun ajiya da kuma hotunan fasfo wadanda ba na gaskiya ba ne don karbar kudin.

Nurudeen ya bayyana cewa wadanda ake tuhumar sun aikata laifin ne tsakanin shekarar 2019 zuwa Disamba 2022 a bankin Think Finance Microfinance Bank dake cikin garin FESTAC.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

A cewar Nurudeen laifuffukan sun ci karo da juna kuma ana hukunta su a karkashin sashe na 314, 325 (1) da 287 (a) (b) (e) na dokar laifuka ta Jihar Legas, 2015.

A wani bangare na tuhume-tuhumen ya karanto cewa, “Kai, Ojimi Ayodeji, Isaac Eddy, jami’in bayar da lamuni, Joseph Setonji, Juwon Irinyemi da sauran su a yanzu, tsakanin shekarar 2019 da Disamba 2022, a bankin Think Finance Microfinance Bank, garin FESTAC, Legas, a gundumar Legas, kun hada kai a tsakanin da juna don aikata laifukan damfara kuma ta haka ne kuka aikata laifin da zai sa hukunta ku a karkashin sashe na 325 (1) na dokar laifuka ta Jihar Legas, a shekarar 2015.

“Kai, Ojimi Ayodeji, shugaban kula da kadara, Isaac Eddy, jami’in bayar da lamuni, Joseph Setonji, Juwon Irinyemi, da sauran su a yanzu, tsakanin 2019 da Disamba 2022, a bankin Think Finance Microfinance Bank, FESTAC Town, Legas, a cikin Kotun Majistare ta Legas, sun yi zamba ta ware rancen Naira miliyan 150 ga wadanda kuka samar da lambarsu ta asusus da BBN da sunan asusun ajiya da hotunan fasfo wadanda ba na gaskiya ba, wakilcin da kuka san karya ne amma kuka aikata laifin, hakan ya sanya za a hukunta ku a karkashin sashe na 314 na dokar laifuka ta Legas, da aka gabatar a Jihar a 2015.”
Sai dai wadanda ake tuhumar sun ki amsa laifin da ake tuhumar su da shi.
Lauyan wadanda ake kara, Barista Ola, ya roki kotun da ta bayar da belinsu cikin mafi sassaucin ra’ayi.

Ba tare da adawa daga masu gabatar da kara ba, Nwaka ya amince da bayar da belinsu a kan kudi Naira miliyan 2 kowannen su tare da mutum hudu da za su tsaya musu.
Ya ce kowane wanda zai tsaya musu zai gabatar da takardar shaidar biyan haraji na shekaru uku da kotu za ta tantance, sannan ta dage sauraron karar har zuwa ranar 16 ga Agusta, 2023.

Bankin kasuwanci
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.