ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Nau’in Kwadi Da Macizai Sun Haddasa Asarar Dala Biliyan 16 A Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Kwadi

Kwararru a harkar kimiyya da ke tattara asarar da wasu mugayen kwari suka haifar a fadin duniya sun gano wasu halittu biyu da suka jawo asara fiye da sauran.

Nau’in kwado dan Amurka da ake kira American bullfrog a Turance da kuma jan maciji – da ake kira brown tree snake a Turance, sun haddasa asarar kudin da suka kai Dala biliyan 16 da 300,000, kwatankwacin Naira tiriliyan shida a fadin duniya tun daga shekarar 1986.

  • Nijeriya Ta Yi Barazanar Ficewa Daga Kungiyar ECOWAS
  • Wang Yi Ya Yi Cikakken Bayani Kan Matsayar Sin Game Da Yankin Taiwan

kari a kan albarkatun tsirrai da suka lalata, mugayen dabbobin sun kuma lalata amfanin gona sannan suka haifar da katsewar wutar lantarki.

ADVERTISEMENT

Masu bincike na fatan abin da suka gano zai taimaka wajen tara kudade don dakile ayyukan mugayen dabbobi a nan gaba.

Cikin rahoton binciken da suka wallafa, masana kimiyya sun dora wa jan macijin alhakin haifar da barnar Dala biliyan 10.3 jimilla, ta hanyar karade wasu tsibirai a yankin Pacific.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

A yankin Guam, inda sojojin Amurka suka kaddamar da macijin a karnin da ya gabata, ‘ya’yan nau’insa sun haddasa daukewar wutar lantarki da yawa saboda suna makalkalewa kan wayoyin lantarki tare da haddasa asara mai yawan gaske.

Akwai nau’in wannan maciji kusan akalla miliyan biyu a dan karamin tsibirin, inda wasu alkaluman ke cewa akwai akalla guda 20 a tsawon kowace girman eka na dajin Guam.

Ana ganin dazukan da ke tsibirai sun fi fuskantar hatsarin muggan dabbobi, inda suke yawan saka sauran dabbobin da ke rayuwa a wurin cikin hadarin karewa a bankasa.

A nahiyar Turai, akwai dandazon kwadi da ke bukatar a kula da su da kyau.

Don dakile hadarin kwadin, wadanda kan yi tsawon da ya kai na kusan kafa daya da kuma nauyin rabin kilo, sun tilasta wa hukumomi dasa shingaye a wuraren kiwo.

Saka shinge a wuaren kiwo biyar kawai don hana kwadin guduwa ya jawo wa hukumomin Jamus kashe kudi Yuro 270,000, kwatankwacin Naira miliyan 114, kamar yadda wani tsohon bincike na Tarayyar Turai ya bayyana.

Rahotanni na cewa dabbar na cin kusan komai, ciki har da ‘yan uwansa kwadi.

Ana zargin wani nau’in na kwado da aka fi sani da haddasa asara ta wata hanyar daban: karar kukansu ta sa darajar gidajen da ke kusa da su ta karye.

Masu bincike na fatan sakamakon abin da suka gano zai karfafa wa hukumomi gwiwa wajen samar da kudaden dakile barazanar dabbobi mugaye.

Kwadi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

MASU ALAKA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Al'ajabi

Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano

January 21, 2026
Next Post
Luguden Ruwan Wuta Ya Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

Luguden Ruwan Wuta Ya Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Da Turkiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Haɗin Gwuiwa Don Bunƙasa Harkar Ma’adinai

Nijeriya Da Turkiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Haɗin Gwuiwa Don Bunƙasa Harkar Ma’adinai

June 6, 2026
Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

June 6, 2026
NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

June 6, 2026
Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

June 6, 2026
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

June 5, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.