ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Nau’in Kwadi Da Macizai Sun Haddasa Asarar Dala Biliyan 16 A Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Kwadi

Kwararru a harkar kimiyya da ke tattara asarar da wasu mugayen kwari suka haifar a fadin duniya sun gano wasu halittu biyu da suka jawo asara fiye da sauran.

Nau’in kwado dan Amurka da ake kira American bullfrog a Turance da kuma jan maciji – da ake kira brown tree snake a Turance, sun haddasa asarar kudin da suka kai Dala biliyan 16 da 300,000, kwatankwacin Naira tiriliyan shida a fadin duniya tun daga shekarar 1986.

  • Nijeriya Ta Yi Barazanar Ficewa Daga Kungiyar ECOWAS
  • Wang Yi Ya Yi Cikakken Bayani Kan Matsayar Sin Game Da Yankin Taiwan

kari a kan albarkatun tsirrai da suka lalata, mugayen dabbobin sun kuma lalata amfanin gona sannan suka haifar da katsewar wutar lantarki.

ADVERTISEMENT

Masu bincike na fatan abin da suka gano zai taimaka wajen tara kudade don dakile ayyukan mugayen dabbobi a nan gaba.

Cikin rahoton binciken da suka wallafa, masana kimiyya sun dora wa jan macijin alhakin haifar da barnar Dala biliyan 10.3 jimilla, ta hanyar karade wasu tsibirai a yankin Pacific.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

A yankin Guam, inda sojojin Amurka suka kaddamar da macijin a karnin da ya gabata, ‘ya’yan nau’insa sun haddasa daukewar wutar lantarki da yawa saboda suna makalkalewa kan wayoyin lantarki tare da haddasa asara mai yawan gaske.

Akwai nau’in wannan maciji kusan akalla miliyan biyu a dan karamin tsibirin, inda wasu alkaluman ke cewa akwai akalla guda 20 a tsawon kowace girman eka na dajin Guam.

Ana ganin dazukan da ke tsibirai sun fi fuskantar hatsarin muggan dabbobi, inda suke yawan saka sauran dabbobin da ke rayuwa a wurin cikin hadarin karewa a bankasa.

A nahiyar Turai, akwai dandazon kwadi da ke bukatar a kula da su da kyau.

Don dakile hadarin kwadin, wadanda kan yi tsawon da ya kai na kusan kafa daya da kuma nauyin rabin kilo, sun tilasta wa hukumomi dasa shingaye a wuraren kiwo.

Saka shinge a wuaren kiwo biyar kawai don hana kwadin guduwa ya jawo wa hukumomin Jamus kashe kudi Yuro 270,000, kwatankwacin Naira miliyan 114, kamar yadda wani tsohon bincike na Tarayyar Turai ya bayyana.

Rahotanni na cewa dabbar na cin kusan komai, ciki har da ‘yan uwansa kwadi.

Ana zargin wani nau’in na kwado da aka fi sani da haddasa asara ta wata hanyar daban: karar kukansu ta sa darajar gidajen da ke kusa da su ta karye.

Masu bincike na fatan sakamakon abin da suka gano zai karfafa wa hukumomi gwiwa wajen samar da kudaden dakile barazanar dabbobi mugaye.

Kwadi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
Next Post
Luguden Ruwan Wuta Ya Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

Luguden Ruwan Wuta Ya Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.