• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Sanatoci Za Su Kalubalanci Nasarar Zaben Akpabio A Kotu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Akpabio

Har zuwa yanzu dai tsugume ba ta kare ba kan shugabancin majalisar kasa ta 10 yayin da wasu fusatattun Sanatoci suka kammala shirye-shiryen garzayawa Kotu domin kalubalantar nasarar da Godswill Akpabio ya samu a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Kamar yadda LEADERSHIP ta gano cewa, ‘Yan majalisar sun nuna rashin gamsuwarsu kan kuri’un da aka yi amfani da su a wajen zaben shugaban majalisar dattawan da zargin an tabka magudi a zaben.

  • Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa
  • An Rantsar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisar Dattawa Na 13

An kuma gano bayan zaben na majalisar dattawa ta 10, wasu Sanatoci na shirin yin tutsu ga jam’iyyar APC da barazanar ficewa daga cikinta.

Wata majiya daga majalisar ta shaida wa wakilinmu cewa Sanatoci 22 sun gama shirin sauya sheka zuwa wasu Jam’iyyun siyasa, ta yadda ‘yan adawa za su samu rinjaye a zauren majalisar.

Muddin wannan shirin ya tabbata, Jam’iyyun adawa za su samu mambobi 72 (Sanatoci) yayin da kuma APC za ta samu ragowar Sanatoci 37 kacal.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Sai dai kuma tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya karyata zargin da wasu abokan aikinsa sanatoci suka yi, tare da cewa ba wasa Sanatocin suka yi ba a ranar 13 ga watan Yuni da suka zabi Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa.

An gano Kalu wani faifayin bidiyo, ya ce, “A zahirin gaskiya zaben majalisar dattawa ya gudana bisa inganci. Sanata Akpabio ya ci zabensa. An yi bisa inganci kuma sahihin zabe.”

Kalu ya ce, ba a taba yin majalisa biyu ba, majalisa daya ce kuma sun riga sun kafata a ranar 13 ga watan Yuni tare da zaben shugaba da mataimaki.

To sai dai Sanatocin da suka zanta da wakilinmu sun yi watsi da ikirarin Kalu, suna masu hakikancewa kan ba za su bari sabon shugaban majalisar ya kammala wa’adinsa ba.

Wasu Sanatoci biyu daga arewa maso gabas masu ra’ayi irin fusatattun Sanatocin, sun ce, an malkwada zaben ne kawai domin a dakile takarar Sanata Abdul’aziz Yari.

Daya daga cikin Sanatocin wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya ce, “Duk da an yi zabe har ma Akpabio ya samu nasara, amma akwai tulin ayoyin tambaya a kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Next Post
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi - Matar Gwamnan Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.