• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana damuwarta ta yadda wasu ‘yan siyasa suke daukar zaben 2023 a matsayin na ko a mutu, ko a yi rai.

Babban jami’an hulda da jama’a na hukumar INEC, Festus Okoye, shi ya bayyana hakan a ranar Litinin da ta gabata a Abuja lokacin kaddamar da tawagar tattauna rikicin zabe, wanda cibiyar bankasa harkokin dimokuradiyya (CDD) ta shirya.

  • Ya Kashe Yayansa Kan Kudin Wutar Lantarki Naira 1,500 A Anambra
  • Miji Ya Ce Wa Matarsa In Kika Fita Ta Kofa Kin Saku, Sai Ta Fice Ta Taga, Shin Ta Saku?

Ya ce, “Sakamakon yadda ‘yan siyasa suka dauki zaben 2023, na ko a mutu, ko a yi rai kamar dai yaki mai dogon zango,” in ji Okoye.

Ya kara da cewa hukumar INEC tana jin dadin yadda ‘yan jarida suke watsa labaranta, amma ya dace a dunga samun sahihan labarai daga hukumar ta hanyar tuntubarta.

“Hukumar INEC tana da kyakkyawan alaka a tsakaninta da ‘yan jarida wajen bayyana wa al’umma labaranta, amma ana samun labarai karya wanda ake yada wa mutane.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Kamar yadda muke samun karuwar labaran karya da ake jingina wa hukumar, mun dauki matakin yaki da lamarin ta hanyar tsaftace labaran harkokin siyasa musamman ga wadanda suka tsaya takara.”

Ya yaba wa cibiyar CDD bisa kirkiro wannan tsari a lokacin da ya dace domin inganta harkokin hukumar.

Ya ce, “Cibiyar CDD ta nuna cewa ita ba jagoran kungiyoyin farafen huda kadai ba ce, ita mai bunkasa harkokin dimokuradiyyar Nijeriya ce, domin haka muna gode musu kan damuwa wajen abubuwan da suka shafi kasa ta hanyar gudanar da bincike.”

Okoye ya ce ‘yan Nijeriya za su zabe ‘yan takara a mazabe 1,491, ciki har da mazabun ‘yan majalisar dattawa 109 da na wakilai 360 da kuma majalisar dokokin jiha 993 da suke neman kujeru a zaben 2023.

“A kokarinta na shirye-shirye, INEC ta dauki ma’aikata da horar da jami’anta da za a tura su runfunar zabe guda 176,846 da cibiyoyin zabe 8,809 da ke cikin kananan hukumomi guda 774 a fadin jihohi 37 ciki har da Abuja.

“Wannan su suka sa aka kara daukan matakai na tabbatar da an buga tare da bayar da katin zabe ga al’umma kafin babban zaben 2023.

“An gudanar da wannan aikin ne saboda ana tsammanin mutum miliyan 95 za su yi zaben 2023, wanda ya zarce sama da miliyan 20 na yawan kasashe 14 da ke fadin yammacin Afirka.

“Ana tsammanin hukumar ta gudanar da wadannan gagarumin aiki da kyau duk da irin kalubalen da kasar take fuskanta, musamman rashin kyau yanayi na zirga-zirga,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023INECJam'iyyaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin ‘Yan Wasa Mafi Tsada A Firimiyar Ingila

Next Post

Fasto Ya Dirka Wa ‘Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Zaben 2023
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Fasto Ya Dirka Wa ‘Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

Fasto Ya Dirka Wa 'Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 14, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.