• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

by Naziru Adam Ibrahim
11 months ago
in Manyan Labarai
0
WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya yi wa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, tayin muƙamin jakada a ɗaya daga ƙasashen Afrika, kamar yadda wata majiya mai tushe ta tabbatar.

Kazalika, majiyar ta ce shugaban ya wakilta shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya sanar da Ganduje.

  • Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa
  • Shugaban Majalisa Ya Janye Ƙudirin Dokar Dauri Ga Wanda Ya Ki Rera Taken Nijeriya

An naɗa Ganduje, a matsayin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa a ranar 3 ga watan Agusta 2023, biyo bayan murabus ɗin da Abdullahi Adamu.

A cewar majiyar Akpabio, ya shaida wa Ganduje tayin shugaban ƙasar na da nufin ceto shi daga shari’ar cin hanci da rashawa da yake fuskanta a Kano game da faifan bidiyon Dala na shekarar 2018.

Ya ce bidiyon ya janyo masa ba’a da gori a bainar jama’a, tare da matarsa da ɗansa da kuma sauran masu hannu cikin lamarin na sama da Naira biliyan 50.

Labarai Masu Nasaba

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Sai dai wata majiya, ta ce Ganduje ya ƙi amincewa da tayin, inda ya bayyana cewa zargin ƙarya ne, kuma zai yi nasara a shari’arsa a kotu wanda shugaban Tinubu da kansa ya sanar da Ganduje shiri na diflomasiyya tare da ba shi damar zaɓar wata ƙasa a Afirka.

Wata majiya ta kusa da Ganduje ta ce abin da shugaba Tinubu, ya fi so shi ne ya naɗa shi Jakadan Nijeriya a ƙasar Chadi, duba da cewar ya taɓa yin aiki a Ndjamena a matsayin babban sakataren hukumar kula da tafkin Chadi tsakanin 2009 zuwa 2011.

Jaridar Daily Nigeria ta ruwaito cewa kwanaki kaɗan bayan Shugaba Tinubu ya sanar da matakin ga Ganduje, an aike masa da wasiƙar wa’adi game da buƙatar ya gudanar da babban taron majalisar jam’iyyar APC na ƙasa.

Wasikar mai ɗauke da kwanan wata 9 ga watan Agusta, da sa hannun Shugaban Hadiman Tinubu, Femi Gbajabiamila, ta sanar da Ganduje cewa shugaban ƙasa zai samu halartar taron Majalisar Jam’iyyar a ranar 8 zuwa 19 ga Satumba, 2024.

Ko da aka tuntuɓi mai magana da yawun Ganduje, Edwin Olofu, ya ce mai gidansa bai yi masa bayani kan batun ba amma ya tabbatar da amincewar shugaban ƙasa na a gudanar da babban taron jam’iyyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCChadiGandujeJakadaTaroTayin MuƙamiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa

Next Post

KANSIEC Ta Sanya 10m A Matsayin Kuɗin Fom Na Takarar Ciyaman A Kano

Related

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

13 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

15 hours ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

19 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

21 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

1 day ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

2 days ago
Next Post
KANSIEC Ta Sanya 10m A Matsayin Kuɗin Fom Na Takarar Ciyaman A Kano

KANSIEC Ta Sanya 10m A Matsayin Kuɗin Fom Na Takarar Ciyaman A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.