• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya kai karar shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa daukaka dan majalisar jiharsa, Ikenga Imo Ugochinyere wajen ba shi kwamiti mai gwabi a cikin gwamnatin jam’iyyar APC. 

Uzodinma ya bayyana rashin jin dadinsa ga Abbas wajen martaba Ugochinyere, wanda ya kasance dan majalisa a karkashin tutur jam’iyyar PDP, na danka masa shugabancin kwamitin man fetur (da aka tace).

  • Remi Tinubu Ta Bada Tallafin Naira Miliyan N500 Ga Iyalai 500 Da Rikici Ya Shafa A Jihar Filato

An bayyana cewa Uzodinma wanda ya kasance shugaban kungiyar gwamnonin APC ya kalubalance nadi bokin hamayyarsa shugaban kwamitin majalisa mai gwabi tun loacin da aka sanar da nadin.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa shugaban majalisar wakilai Abbas ya fusata Uzo-dinma wanda yake ganin cewa wannan nadin zai bai wa Ugochinyere shahara a cikin harkokin siyasa.

Bayan haka kuma, an bayyana cewa gwamnan ya dauki nadin dan majalisar a matsayin shugaban kwamitin mai gwabi za sa dan adawa ya kara karfi a siyasance, wanda hakan cin mutunci ne a matsayinsa na gwamnan jihar kuma shugaban kungiyar gwamnonin APC.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Wata majiya da ke kusa da gwamnan ta bayyana cewa, lallai gwamnan ya yi matukar fusata da nadin Ugochinyere wanda hakan zai taba kimarsa a matsayinsa na gwamnan Jihar Imo.

A cewar wata majiyar, Uzodinma ya damu sosai na nadin Ugochinyere shugabancin kwamitin mai gwabi a zauren majalisar wakilai na tarayya, wanda hakan zai kara wa ‘yan adawa karfi a cikin harkokin siyasa.

Duk da dai kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Jihar Nasarawa ta soke zaben Ugochinyere, dan majalisar ya daukaka kara na kalubalantar hukuncin a kotun daukaka kara.

Ugochinyere zai ci gaba da zama dan majalisar wakilai har sai kotun daukaka kara ta zantar da hukunci.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Uzodinma ya yi kokarin shawo kan Abbas kan ya janye nadin.

An samu rahoton da ke cewa shugaban majalisar wakilan ya yi watsi da bukatar gwamnan.

LEADERSHIP ta kuma kara da cewa tuni Uzodinma ya kai karar Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu kan wannan nadin.

Har ila yau, a nasa martanin, Ugochinyere ya bukaci Uzodinma ya cire Abbas daga ciki siyasar Jihar Imo.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, dan majalisar da ke cikin rudani ya bayyana cewa ba sai ya bukaci goyon bayan Abbas ba wajen murkushe Uzodinma a zabe mai zuwa a jihar.

Ya siffanta Uzodimma a matsayin karamin kwaro a siyasa. Ya ce, “Za mu mur-kushe Uzodinma a zaben gwamna a watan Nuwamba kamar yadda muka yi a zaben watan Mayu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnonimajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Kori Kwamishina Kan Kalaman Barazana Ga Alkalai

Next Post

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.