• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wutar Lantarki Ta Kashe Mutum 112, Wasu 108 Sun Jikkata A 2024

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
Wutar lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kalla ‘yan Nijeriya mutum 112 ne suka rasa rayukansu a sakamakon hadurran da suke da alaka da wutar lantarki a shekarar 2024, kamar yadda rahoton zango da hukumar kula da wurin wutar lantarki a Nijeriya (NERC) ta fitar.

Rahoton ya kuma nuna cewa wadannan adadin mutuwar ya faru ne a cikin hadurra guda 228 da aka samu wanda ya jikkata wasu karin mutum 108.

  • Gobara Ta Ƙone Shaguna 3 Da Kayayyaki Masu Yawan Gaske A Ibadan
  • Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Jerin mace-macen sun kunshi cewa mutum 23 da suka mutu sakamakon hadurra 55 da suka faru a farkon zangon shekarar 2024, inda wasu 31 kuma suka jikkata. A zango na biyu kuma an samu rahotonnin hatsarin wutar lantarki guda 63, inda a cikin wannan aka samu matattu 34 da wasu 17 da suka raunata.

Sai kuma a zango na uku da aka samu hatsarin wutar lantarki guda 56 da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 29 da jikkata wasu 38, sai kuma a zango na karshe aka samu faruwar hatsarin sau 54 da ya janyo asarar rayuka 23 da jikkata wasu 19.

Rahoton ya nuna cewa mutum 33 sun rasa rayukansu ne sakamakon hadewar wayoyin lantarki, yayin da wannan matsalar ta jikkata wasu 13.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Haka zalika, mutuwar mutane 33 da jikkata 54 sun faru ne sakamakon munanan ayyuka na ganganci da rashin yanayi mai kyau, yayin da yin aiki ba bisa ka’ida ba ya kai ga mutuwar 23 da jikkata shida.

Masu barnatawa da lalata kayan wuta sun janyo mutuwar mutane 18 da jikkata wasu 7, sai kuma hatsarin fadowa daga sama ya janyo mutuwar mutum daya da jikkata wasu 18.

A Nijeriya dai sama da shekaru ana fama da matsalar rasa rayukansu da jikkata mutane da dama daga hadurran da suka shafi na wutar lantarki kuma wannan mafi akasari na faruwa ne sakamakon amfani da kayan wuta marasa inganci ko marasa kyau, karancin amfani da kayayyakin kariya, ayyukan masu lalata kayan wuta da kuma yin gina kusa ko a kasar layukan wutar lantarki da dai sauran matsalolin.

Da yake zantawa da manema labarai, Manajan Daraktan Hukumar Kula da Ayyukan Wutar Lantarki ta Nijeriya (NEMSA), Injiniya Aliyu Tahir, ya ce binciken da aka yi a kan dukkan hadurrukan da suka wakana ya zuwa yanzu ya nuna cewa da yawa daga cikinsu wadanda lamarin ya shafa sun hada da ma’aikatan kamfanonin samar da wutar lantarki.

Injiniya Tahir ya lura kan cewa hadurran mafi yawansu sun faru ne sakamakon rashin kin bin ka’idojin aiki da matakan kariya a yayin gudanar da aiki da aikin kula da lamuran wuta.

“Muna ganin yadda ma’aikata ke aiki kan layukan wutar lantarki ba tare da kayan aikin kariya na ma’aikata ba.

“Muna kuma ganin yadda wasu ke hanzari da gaggawa yayin aikin gyara wuta. Wannan fa wutar lantarki ne. Wutar lantarki na tattare da abubuwa masu hatsari sosai, wadannan hatsarin suna kuma shafan masu gudanar da aikin, don haka bin matakan kariya da kiyayewa da sanya kwarewa a bangaren aiki ne kawai zai kai ga rage matsalolin nan,” ya shaida.

Ya ce, hukumar tana kan sake nazarta matakan kariya domin tabbatar da kamfanonin wutar lantarki suna bi domin kare kai tare da sahalewa da amincewar NERC.

Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta yi kira ga bangaren shari’a da su tabbatar da daukar nauyin kamfanonin wutar lantarki da aka samu sakamakon mace-macen wutar lantarki a kasar nan.

Da take jawabi yayin wani taron kara wa juna sani da Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) ta shirya a Abuja, ta bayyana fargaba kan mutuwar mutane 112 da suka samu wutar lantarki da kuma jikkata 95 a shekarar 2024 kadai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobara Ta Ƙone Shaguna 3 Da Kayayyaki Masu Yawan Gaske A Ibadan

Next Post

Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

6 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

9 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

9 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

11 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

11 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

12 hours ago
Next Post
Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

Dole Jama'a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta'adda

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.