ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wutar Lantarki Ta Kashe Mutum 112, Wasu 108 Sun Jikkata A 2024

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Wutar lantarki

A kalla ‘yan Nijeriya mutum 112 ne suka rasa rayukansu a sakamakon hadurran da suke da alaka da wutar lantarki a shekarar 2024, kamar yadda rahoton zango da hukumar kula da wurin wutar lantarki a Nijeriya (NERC) ta fitar.

Rahoton ya kuma nuna cewa wadannan adadin mutuwar ya faru ne a cikin hadurra guda 228 da aka samu wanda ya jikkata wasu karin mutum 108.

  • Gobara Ta Ƙone Shaguna 3 Da Kayayyaki Masu Yawan Gaske A Ibadan
  • Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Jerin mace-macen sun kunshi cewa mutum 23 da suka mutu sakamakon hadurra 55 da suka faru a farkon zangon shekarar 2024, inda wasu 31 kuma suka jikkata. A zango na biyu kuma an samu rahotonnin hatsarin wutar lantarki guda 63, inda a cikin wannan aka samu matattu 34 da wasu 17 da suka raunata.

ADVERTISEMENT

Sai kuma a zango na uku da aka samu hatsarin wutar lantarki guda 56 da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 29 da jikkata wasu 38, sai kuma a zango na karshe aka samu faruwar hatsarin sau 54 da ya janyo asarar rayuka 23 da jikkata wasu 19.

Rahoton ya nuna cewa mutum 33 sun rasa rayukansu ne sakamakon hadewar wayoyin lantarki, yayin da wannan matsalar ta jikkata wasu 13.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Haka zalika, mutuwar mutane 33 da jikkata 54 sun faru ne sakamakon munanan ayyuka na ganganci da rashin yanayi mai kyau, yayin da yin aiki ba bisa ka’ida ba ya kai ga mutuwar 23 da jikkata shida.

Masu barnatawa da lalata kayan wuta sun janyo mutuwar mutane 18 da jikkata wasu 7, sai kuma hatsarin fadowa daga sama ya janyo mutuwar mutum daya da jikkata wasu 18.

A Nijeriya dai sama da shekaru ana fama da matsalar rasa rayukansu da jikkata mutane da dama daga hadurran da suka shafi na wutar lantarki kuma wannan mafi akasari na faruwa ne sakamakon amfani da kayan wuta marasa inganci ko marasa kyau, karancin amfani da kayayyakin kariya, ayyukan masu lalata kayan wuta da kuma yin gina kusa ko a kasar layukan wutar lantarki da dai sauran matsalolin.

Da yake zantawa da manema labarai, Manajan Daraktan Hukumar Kula da Ayyukan Wutar Lantarki ta Nijeriya (NEMSA), Injiniya Aliyu Tahir, ya ce binciken da aka yi a kan dukkan hadurrukan da suka wakana ya zuwa yanzu ya nuna cewa da yawa daga cikinsu wadanda lamarin ya shafa sun hada da ma’aikatan kamfanonin samar da wutar lantarki.

Injiniya Tahir ya lura kan cewa hadurran mafi yawansu sun faru ne sakamakon rashin kin bin ka’idojin aiki da matakan kariya a yayin gudanar da aiki da aikin kula da lamuran wuta.

“Muna ganin yadda ma’aikata ke aiki kan layukan wutar lantarki ba tare da kayan aikin kariya na ma’aikata ba.

“Muna kuma ganin yadda wasu ke hanzari da gaggawa yayin aikin gyara wuta. Wannan fa wutar lantarki ne. Wutar lantarki na tattare da abubuwa masu hatsari sosai, wadannan hatsarin suna kuma shafan masu gudanar da aikin, don haka bin matakan kariya da kiyayewa da sanya kwarewa a bangaren aiki ne kawai zai kai ga rage matsalolin nan,” ya shaida.

Ya ce, hukumar tana kan sake nazarta matakan kariya domin tabbatar da kamfanonin wutar lantarki suna bi domin kare kai tare da sahalewa da amincewar NERC.

Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta yi kira ga bangaren shari’a da su tabbatar da daukar nauyin kamfanonin wutar lantarki da aka samu sakamakon mace-macen wutar lantarki a kasar nan.

Da take jawabi yayin wani taron kara wa juna sani da Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) ta shirya a Abuja, ta bayyana fargaba kan mutuwar mutane 112 da suka samu wutar lantarki da kuma jikkata 95 a shekarar 2024 kadai.

Lantarki
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Lantarki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

Dole Jama'a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta'adda

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.