ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wutar Lantarki Ta Kashe Mutum 112, Wasu 108 Sun Jikkata A 2024

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Wutar lantarki

A kalla ‘yan Nijeriya mutum 112 ne suka rasa rayukansu a sakamakon hadurran da suke da alaka da wutar lantarki a shekarar 2024, kamar yadda rahoton zango da hukumar kula da wurin wutar lantarki a Nijeriya (NERC) ta fitar.

Rahoton ya kuma nuna cewa wadannan adadin mutuwar ya faru ne a cikin hadurra guda 228 da aka samu wanda ya jikkata wasu karin mutum 108.

  • Gobara Ta Ƙone Shaguna 3 Da Kayayyaki Masu Yawan Gaske A Ibadan
  • Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Jerin mace-macen sun kunshi cewa mutum 23 da suka mutu sakamakon hadurra 55 da suka faru a farkon zangon shekarar 2024, inda wasu 31 kuma suka jikkata. A zango na biyu kuma an samu rahotonnin hatsarin wutar lantarki guda 63, inda a cikin wannan aka samu matattu 34 da wasu 17 da suka raunata.

ADVERTISEMENT

Sai kuma a zango na uku da aka samu hatsarin wutar lantarki guda 56 da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 29 da jikkata wasu 38, sai kuma a zango na karshe aka samu faruwar hatsarin sau 54 da ya janyo asarar rayuka 23 da jikkata wasu 19.

Rahoton ya nuna cewa mutum 33 sun rasa rayukansu ne sakamakon hadewar wayoyin lantarki, yayin da wannan matsalar ta jikkata wasu 13.

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Haka zalika, mutuwar mutane 33 da jikkata 54 sun faru ne sakamakon munanan ayyuka na ganganci da rashin yanayi mai kyau, yayin da yin aiki ba bisa ka’ida ba ya kai ga mutuwar 23 da jikkata shida.

Masu barnatawa da lalata kayan wuta sun janyo mutuwar mutane 18 da jikkata wasu 7, sai kuma hatsarin fadowa daga sama ya janyo mutuwar mutum daya da jikkata wasu 18.

A Nijeriya dai sama da shekaru ana fama da matsalar rasa rayukansu da jikkata mutane da dama daga hadurran da suka shafi na wutar lantarki kuma wannan mafi akasari na faruwa ne sakamakon amfani da kayan wuta marasa inganci ko marasa kyau, karancin amfani da kayayyakin kariya, ayyukan masu lalata kayan wuta da kuma yin gina kusa ko a kasar layukan wutar lantarki da dai sauran matsalolin.

Da yake zantawa da manema labarai, Manajan Daraktan Hukumar Kula da Ayyukan Wutar Lantarki ta Nijeriya (NEMSA), Injiniya Aliyu Tahir, ya ce binciken da aka yi a kan dukkan hadurrukan da suka wakana ya zuwa yanzu ya nuna cewa da yawa daga cikinsu wadanda lamarin ya shafa sun hada da ma’aikatan kamfanonin samar da wutar lantarki.

Injiniya Tahir ya lura kan cewa hadurran mafi yawansu sun faru ne sakamakon rashin kin bin ka’idojin aiki da matakan kariya a yayin gudanar da aiki da aikin kula da lamuran wuta.

“Muna ganin yadda ma’aikata ke aiki kan layukan wutar lantarki ba tare da kayan aikin kariya na ma’aikata ba.

“Muna kuma ganin yadda wasu ke hanzari da gaggawa yayin aikin gyara wuta. Wannan fa wutar lantarki ne. Wutar lantarki na tattare da abubuwa masu hatsari sosai, wadannan hatsarin suna kuma shafan masu gudanar da aikin, don haka bin matakan kariya da kiyayewa da sanya kwarewa a bangaren aiki ne kawai zai kai ga rage matsalolin nan,” ya shaida.

Ya ce, hukumar tana kan sake nazarta matakan kariya domin tabbatar da kamfanonin wutar lantarki suna bi domin kare kai tare da sahalewa da amincewar NERC.

Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta yi kira ga bangaren shari’a da su tabbatar da daukar nauyin kamfanonin wutar lantarki da aka samu sakamakon mace-macen wutar lantarki a kasar nan.

Da take jawabi yayin wani taron kara wa juna sani da Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) ta shirya a Abuja, ta bayyana fargaba kan mutuwar mutane 112 da suka samu wutar lantarki da kuma jikkata 95 a shekarar 2024 kadai.

Lantarki
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
Lantarki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Lantarki
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Next Post
Dole Jama’a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

Dole Jama'a Su Marawa Sojoji  Baya Don Samun Nasara A Yaƙi Da Ƴan Ta'adda

LABARAI MASU NASABA

Lantarki

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.