• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Da Joe Biden Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Da Joe Biden Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna da takwaransa na Amurka Joe Biden a jiya Talata ta wayar tarho, bisa bukatar shugaba Biden. Shugabannin biyu sun yi tattaunawa mai zurfi da musayar ra’ayi kan dangantakar kasashensu da batutuwan da ke jan hankulansu.

Shugaba Xi ya bayyana cewa, ganawarsa da shugaba Biden a watan Nuwamban bara a birnin San Francisco, ya bude wata mahangar makomarsu. Ya ce cikin watannin da suka gabata, jami’an kasashen biyu sun aiwatar da matsayar da suka cimma sahihanci. Kuma dangantakar Sin da Amurka ta fara daidaituwa, sannan al’ummomin kasashen biyu da ma na kasa da kasa na maraba da hakan. Ya ce a daya bangaren, abubuwan dake yin mummunan tasiri kan dangantakarsu na karuwa, don haka akwai bukatar bangarorin biyu su mayar da hankali kan su.

  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Fadada Yankunan Tudu Na Teku Da Take Iko Da Su
  • Sin Ta Mai Da Martani Ga Yadda Amurka Ta Gyara Matakin Kayyade Fitar Da Kayayyakin Sassan Laturoni Zuwa Ketare

Shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, batun Taiwan shi ne iyaka ta farko da bai kamata a tsallake ba a dangantakar kasashen biyu. Ya ce kasar Sin ba za ta nade hannu tana kallon ayyukan ‘yan aware masu neman ‘yancin yankin da tallafi da goyon bayan da ake ba su daga waje ba.

A nasa bangaren, shugaba Biden ya ce dangatakar Sin da Amurka ita ce mafi tasiri a duniya. Kuma ci gaban dangantakar da aka samu bayan ganawarsu ta San Francisco, ya nuna cewa bangarorin biyu za su iya inganta hadin gwiwarsu tare da hakuri da bambance-bambancen dake akwai tsakaninsu.

Joe Biden ya kuma nanata cewa, Amurka ba ta neman tada sabon yakin cacar baka, kuma ba ta da muradin sauya tsarin kasar Sin, haka kuma kawancen da take yi ba ya nufin yi wa Sin taron dangi. Kazalika, Amurka ba ta goyon bayan ‘yancin yankin Taiwan, kuma ba ta neman tada rikici tsakaninta da Sin. Bugu da kari, ya ce Amurka tana goyon bayan manufar Sin daya tak a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya yi karin haske a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau, game da tattaunawa ta wayar tarho, tsakanin shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, kan batutuwan sashen tudun ruwa na Ren’aijiao, da yankin Hong Kong, da jihar Xinjiang, da ta Xizang da sauransu.

Game da batun sashen tudun ruwa na Ren’aijiao, Wang Wenbin ya bayyana cewa, a yayin tattaunawar, Sin ta jaddada cewa, tana da ikon mallakar tsibiran Nansha, da yankin teku dake dab da su, wadanda suka hada da tsibirai da sassan tudun ruwa, da yankunan rairayi, ciki har da sashen tudun ruwa na Ren’aijiao.

Wannan batu dai ya biyo bayan yadda bangaren kasar Philippines ya yi ta sabawa alkawarin da ya dauka, ta hanyar yunkurin kafa sashensa na dindindin a kan tsibirai, da sassan tudun ruwa na kasar Sin da babu mutune a kansu, da nufin sace ikon mallakar sashen tudun ruwan Ren’aijiao. Bangaren Sin na ganin Amurka ba ta da nasaba da wannan batu na yankin kudancin tekun kasar Sin, don haka bai kamata ta tsoma baki cikin batun Sin da Philippines ba.

Game da batun jihar Xinjiang da ta Xizang, Wang Wenbin ya jaddada cewa, batun Xinjiang da Xizang, batu ne na cikin gidan kasar Sin. Kaza lika kasar Sin na dora muhimmanci sosai kan kare hakkin dan Adam. Ya ce, jama’ar kasar ne ke da ikon bayyana ra’ayinsu kan kare hakkin dan Adam na kasarsu.

A daya bangaren, kasar Sin tana fatan yin mu’amala tare da Amurka, kan batun kare hakkin dan Adam bisa tushen girmama juna, sai dai Sin din ba za ta amince da duk wani nau’in aiki na tsoma baki cikin harkokin cikin gidanta bisa hujjar kare hakkin dan Adam ba. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha&Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Next Post

Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

11 hours ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

12 hours ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

14 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

16 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

16 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

1 day ago
Next Post
Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

Babban Yankin Kasar Sin Na Maida Hankali Sosai Kan Bala’ in Girgizar Kasar Da Ya Afkawa Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.