• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Kolin FOCAC

by CGTN Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Kolin FOCAC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Yau Alhamis, an bude taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC na shekarar 2024 a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron, inda ya gabatar da jawabi mai taken “Mu hada kai domin inganta harkokin zamanantarwa, da kuma gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya”.
Cikin jawabinsa, Xi Jinping ya bayyana cewa, kafuwar dandalin FOCAC a shekarar 2000 yana da muhimmanci matuka wajen raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka. Cikin shekaru 24 da suka gabata, kasar Sin da kasashen Afirka sun fahimci juna da goyawa juna baya, lamarin da ya kasance abin koyi wajen kafa sabuwar dangantakar dake tsakanin kasa da kasa.
Xi ya sanar da cewa, za a daga huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da Sin zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, da kuma mai da dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka a matsayin dangantakar gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya a dukkan fannoni cikin sabon zamani.
Xi ya ce, ya kamata kasar Sin da kasashen Afirka su hada kansu domin inganta harkokin neman zamanantarwa a fannoni guda shida, wato neman zamanantarwa cikin yanayin adalci, da neman zamanantarwa mai bude kofa ga waje da cimma moriyar juna, da neman zamanantarwa mai bautawa jama’a, da neman zamanantarwa mai nuna fahimtar juna, da neman zamanantarwa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma neman zamanantarwa ta hanyoyin zaman lafiya da tsaro.
Ya kuma kara da cewa, cikin shekaru 3 masu zuwa, kasar Sin tana fatan yin hadin gwiwa da kasashen Afirka wajen tsara manyan matakan sada zumunci da neman zamanantarwa a fannoni 10, domin zurfafa hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da ba da jagoranci ga kasashe masu tasowa kan harkokin zamanantar da kasashen. Wadannan manyan matakai sun kuma hada da fannonin musayar al’adu, da karuwar cinikayya, da hadin gwiwar tsarin samar da kayayyaki, da bunkasa harkokin sadarwa, da raya hadin gwiwa, da inganta harkokin kiwon lafiya, da raya aikin gona da tallafawa al’umma, da karfafa mu’amala a tsakanin jama’a, da neman bunkasuwa ta hanyar kare muhalli, da kuma inganta ayyukan kiyaye tsaro.
Bugu da kari, ya ce, ba za a bar kowa a baya ba kan hanyar neman zamanantarwa. Bari mu hada kan al’ummomin Sin da Afirka biliyan 2 da miliyan dari 8, domin inganta zamanantarwar dukkanin kasashe maso tasowa ta hanyar zamanantar da Sin da Afirka, gami da samar wa kasashen duniya wata makoma mai haske, wadda take da zaman lafiya da tsaro, da wadata da kuma ci gaba. (Mai Fassara: Maryam Yang)

  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FOCACJawabiSinTaroXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

FOCAC: LEADERSHIP Da CMG Sun Sake Ƙarfafa Alaƙar Haɗin Gwiwa 

Next Post

Yusuf Tuggar: Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Na Haifar Da Alfanu A Fannoni Da Dama

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

17 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

18 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

19 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

20 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

21 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

22 hours ago
Next Post
Yusuf Tuggar: Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Na Haifar Da Alfanu A Fannoni Da Dama

Yusuf Tuggar: Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Na Haifar Da Alfanu A Fannoni Da Dama

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.