ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Kolin FOCAC

by CGTN Hausa
1 year ago
xi

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Yau Alhamis, an bude taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC na shekarar 2024 a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron, inda ya gabatar da jawabi mai taken “Mu hada kai domin inganta harkokin zamanantarwa, da kuma gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya”.
Cikin jawabinsa, Xi Jinping ya bayyana cewa, kafuwar dandalin FOCAC a shekarar 2000 yana da muhimmanci matuka wajen raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka. Cikin shekaru 24 da suka gabata, kasar Sin da kasashen Afirka sun fahimci juna da goyawa juna baya, lamarin da ya kasance abin koyi wajen kafa sabuwar dangantakar dake tsakanin kasa da kasa.
Xi ya sanar da cewa, za a daga huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da Sin zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, da kuma mai da dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka a matsayin dangantakar gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya a dukkan fannoni cikin sabon zamani.
Xi ya ce, ya kamata kasar Sin da kasashen Afirka su hada kansu domin inganta harkokin neman zamanantarwa a fannoni guda shida, wato neman zamanantarwa cikin yanayin adalci, da neman zamanantarwa mai bude kofa ga waje da cimma moriyar juna, da neman zamanantarwa mai bautawa jama’a, da neman zamanantarwa mai nuna fahimtar juna, da neman zamanantarwa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma neman zamanantarwa ta hanyoyin zaman lafiya da tsaro.
Ya kuma kara da cewa, cikin shekaru 3 masu zuwa, kasar Sin tana fatan yin hadin gwiwa da kasashen Afirka wajen tsara manyan matakan sada zumunci da neman zamanantarwa a fannoni 10, domin zurfafa hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da ba da jagoranci ga kasashe masu tasowa kan harkokin zamanantar da kasashen. Wadannan manyan matakai sun kuma hada da fannonin musayar al’adu, da karuwar cinikayya, da hadin gwiwar tsarin samar da kayayyaki, da bunkasa harkokin sadarwa, da raya hadin gwiwa, da inganta harkokin kiwon lafiya, da raya aikin gona da tallafawa al’umma, da karfafa mu’amala a tsakanin jama’a, da neman bunkasuwa ta hanyar kare muhalli, da kuma inganta ayyukan kiyaye tsaro.
Bugu da kari, ya ce, ba za a bar kowa a baya ba kan hanyar neman zamanantarwa. Bari mu hada kan al’ummomin Sin da Afirka biliyan 2 da miliyan dari 8, domin inganta zamanantarwar dukkanin kasashe maso tasowa ta hanyar zamanantar da Sin da Afirka, gami da samar wa kasashen duniya wata makoma mai haske, wadda take da zaman lafiya da tsaro, da wadata da kuma ci gaba. (Mai Fassara: Maryam Yang)

  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka
ADVERTISEMENT
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Next Post
Yusuf Tuggar: Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Na Haifar Da Alfanu A Fannoni Da Dama

Yusuf Tuggar: Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Na Haifar Da Alfanu A Fannoni Da Dama

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.