ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Kolin FOCAC

by CGTN Hausa
2 years ago
xi

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Yau Alhamis, an bude taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC na shekarar 2024 a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron, inda ya gabatar da jawabi mai taken “Mu hada kai domin inganta harkokin zamanantarwa, da kuma gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya”.
Cikin jawabinsa, Xi Jinping ya bayyana cewa, kafuwar dandalin FOCAC a shekarar 2000 yana da muhimmanci matuka wajen raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka. Cikin shekaru 24 da suka gabata, kasar Sin da kasashen Afirka sun fahimci juna da goyawa juna baya, lamarin da ya kasance abin koyi wajen kafa sabuwar dangantakar dake tsakanin kasa da kasa.
Xi ya sanar da cewa, za a daga huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da Sin zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, da kuma mai da dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka a matsayin dangantakar gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya a dukkan fannoni cikin sabon zamani.
Xi ya ce, ya kamata kasar Sin da kasashen Afirka su hada kansu domin inganta harkokin neman zamanantarwa a fannoni guda shida, wato neman zamanantarwa cikin yanayin adalci, da neman zamanantarwa mai bude kofa ga waje da cimma moriyar juna, da neman zamanantarwa mai bautawa jama’a, da neman zamanantarwa mai nuna fahimtar juna, da neman zamanantarwa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma neman zamanantarwa ta hanyoyin zaman lafiya da tsaro.
Ya kuma kara da cewa, cikin shekaru 3 masu zuwa, kasar Sin tana fatan yin hadin gwiwa da kasashen Afirka wajen tsara manyan matakan sada zumunci da neman zamanantarwa a fannoni 10, domin zurfafa hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da ba da jagoranci ga kasashe masu tasowa kan harkokin zamanantar da kasashen. Wadannan manyan matakai sun kuma hada da fannonin musayar al’adu, da karuwar cinikayya, da hadin gwiwar tsarin samar da kayayyaki, da bunkasa harkokin sadarwa, da raya hadin gwiwa, da inganta harkokin kiwon lafiya, da raya aikin gona da tallafawa al’umma, da karfafa mu’amala a tsakanin jama’a, da neman bunkasuwa ta hanyar kare muhalli, da kuma inganta ayyukan kiyaye tsaro.
Bugu da kari, ya ce, ba za a bar kowa a baya ba kan hanyar neman zamanantarwa. Bari mu hada kan al’ummomin Sin da Afirka biliyan 2 da miliyan dari 8, domin inganta zamanantarwar dukkanin kasashe maso tasowa ta hanyar zamanantar da Sin da Afirka, gami da samar wa kasashen duniya wata makoma mai haske, wadda take da zaman lafiya da tsaro, da wadata da kuma ci gaba. (Mai Fassara: Maryam Yang)

  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka
xi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Yusuf Tuggar: Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Na Haifar Da Alfanu A Fannoni Da Dama

Yusuf Tuggar: Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Na Haifar Da Alfanu A Fannoni Da Dama

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.