ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

by CMG Hausa
4 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin ya gabatar da jawabi a taron bikin murnar cika shekaru 25 da dawowar yankin Hong Kong karkashin Jamhuriyar jama’ar kasar Sin da kuma bikin kaddamar da sabuwar gwamnatin yankin ta 6.

Xi Jinping, wanda shi ne shugaban kwamitin koli na JKS, kuma shugaban rundunar sojin kasar, ya taya John Lee, sabon jami’in farko na gwamnatin yankin da manyan jami’ai da mambobin majalisar zartarwar sabuwar gwamnatin yankin murna.

  • Xi Jinping: “Kasa Daya Amma Tsarin Mulki Iri Biyu” Mataki Mai Kyau Na Raya Yankin Hong Kong

Shugaban ya ce aiwatar da manufar “Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu” ta haifar da nasarorin da kowa ke iya gani a yankin HK. Kuma tun bayan dawowarsa karkashin kasar Sin, yankin ya bayar da gagarumar gudunmawa ga bunkasar tattalin arzikin kasar mai dogon zango cikin sauri da kuzari ba tare da tangarda ba.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, HK ya zama wani muhimmin bangare ga ci gaban kasar Sin, wanda ya yi daidai da dabarun raya kasar. Baya ga haka, ya ci gaba da rike matsayinsa na mai karfi da bayar da ’yanci da bude kofarsa, tare kuma da kiyaye dokokin kasa da kasa.

Bugu da kari, shugaba Xi ya ce, yankin HK ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa sabon fagen fadada da zurfafa manufar bude kofa ta kasar Sin a karin bangarori.
Kana, HK ya zama jigon saurin ci gaban bangaren kimiyya da fasaha da kirkire kirkire, haka kuma ya samar da kyakkyawan yanayin kasuwanci da ya kai mizanin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Har ila yau, ya ce, an kare tare da kyautata dokokin da ake amfani da su a yankin, kuma al’ummarsa sun kasance tsintsiya madaurinki daya.

A cewarsa, tsarin demokradiyyar HK da ya dace da manufar “Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu”, da kundin tsarin mulkin yankin, shi ne mafi dacewa wajen kare hakkokin demokradiyya na mazauna yankin da kuma tabbatar da ci gaba da kwanciyar hankalinsa.

Ya ce manufar “Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu”, abu ne da aka ga alfanunsa cikin lokaci mai tsawo, don haka babu dalilin sauya ingantaccen tsari irinsa, haka kuma, dole ne a ci gaba da rungumarsa.

Ban da wannan kuma, jami’an sabon gwamnatin yankin sun yi rantsuwar kama aikinsu a bikin. (Fa’iza Mustapha)

Xi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Hajji 2022: Jirgi Zai Kwashe Maniyyata 162 Ya Bar 238 A Jihar Edo

Hajjin Bana: Ko Hukumar Alhazan Nijeriya Za Ta Kammala Jigilar Maniyyata A Kan Kari?

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.