ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Buhari Ya Dakile Barazanar Da APC Ke Fuskanta A Majalisar Dattawa

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Buhari

Wasu ‘yan majalisar dattawa na jam’iyyar APC guda 22 sun yi barazanar sauya sheka zuwa jam’iyyun PDP da LP da NNPP da dai sauran su, bisa kara fusatasu da aka yi sakamakon zaben fid da gwani da aka kammala.

Ganin haka ne ma ya sa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ranar Talata ya roki sanatocin na APC kan kar su bar jam’iyyar domin kar ta rasa rinjaye a zauren majalisan dattawan Nijeriya.

  • 2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose

Shugaba Buhari ya samu zama da wasu ‘yan majalisan dattawa na APC domin jin irin matsalolin da aka samu a wurin zaben fid da gwani da aka kammala. Ya dai amshi korafinsu tare da tabbatar da cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar za ta bi ba’asi a kan lamarin.

ADVERTISEMENT

Ya bukaci ‘yan majalisan da su ci gaba da kokarinsu wajen ganin shugabancin jam’iyyar APC ya bunkasa kasar nan.

Ya ce, “Na ji dukkan korafe-korafenku kan zaben fid da gwani da aka kammala, zan yi kokarin ganin an share wa kowa hawayensa domin jam’iyyarmu ta ci gaba da iko a zauren majalisan dattawa da kuma babban zaben 2023. Ba za mu taba barin wannan barazanar ba tabbata ba.
“Akwai hanyoyin da za mu bi wajen warware duk wata matsa da ta kunno kai.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Wannan shi ne kyakkywan tsari a cikin dimokuradiyyarmu wanda muke gudanarwa. Tun daga lokacin da aka kammala zaben fid da gwani nake ta samun rahoto na korafe-korafe,” in ji shi.

A cewar mashawarcin shugaban kasa a fannin yada labarai, Femi Adesina, Shugaba Buhari ya sha alwashin karfafa shugabancin jam’iyyar APC ta hanyar yin adalci a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar kafin babban zaben 2023.

Shugaba Buhari ya fada wa sanatocin APC cewa samun nasarar jam’iyyar a babban zabe ya ta’allaka ne da yanayin hadin kan ‘ya’yan jam’iyyar da kaucewa rashin adalci a tsakaninsu.

Sai dai kuma Buhari ya gode wa ‘yan majalisan dattawan bisa bayar da shawaran gudanar da tattaunawa ta yadda za a su damar dinke bakin zaren na matsaloli da suka faru a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a lokacin zaben fid da gwani.

A nasa jawabin, shugaban tawagan kuma babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa a yanzu haka akwai a kalla sanatoci 22 da wasu mambobi na jam’iyyar ba su ji dadin abubuwan da suka faru a zaben fid da gwani da aka kammala ba a jihohinsu ba, saboda an gudanar da wasu lamari ba bisa ka’ida ba, wanda suka yi barazanar sauya sheka zuwa wasu jam’iyyun na daban.

Ya kara da cewa ‘yan majalisan dattawan sun sadaukar da kawunansu wajen ganin jam’iyyar ta bunka a cikin dimokuradiyyar kasar nan. Ya yi kira da shugaban kasa ya kawo daukin gaggawa kan wannan lamari.

Ya ce, “Mai girma shugaban kasa, tabbas a zauren majalisa mun yi aiki tukuru wajen ganin duk manufofinka sun gudana. Muna tabbatar maka da cewa a ko da yaushe muna goyon bayanka,” in ji shi.

Buhari
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.