ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Ko Hukumar Alhazan Nijeriya Za Ta Kammala Jigilar Maniyyata A Kan Kari?

by Sulaiman
4 years ago
NAHCON

Ya zuwa ranar Laraba 29 ga watan Yuni 2022, Hukumar Alhazan Nijeriya NAHCON ta samu nasara jigilar Maniyyata fiye da dubu 20,669 daga cikin kujeru 43,008 da aka ware wa jihohin Nijeriya, wannan kuma babbar nasara ce musamman ganin yadda wa’adin kammala jigilar maniyyata daga sassan duniya zuwa kasa mai tsarki ke kara matsowa, wannan ya sa hukumar alhazai karkashin jagorancin Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ke kara kaimun ganin ta kammala kafin a rufe filin jiragen sama na kasar Saudiya.

An samu kwashe Maiyyatar ne a sawu fiye 38 da jiragen sama suka yi daga jihohi 19 da birnin Abuja da kuma tawagar rundunar sojojin Nijeriya ta kamfanonin jiragen sama guda uku da suka hada da Mad Air; Azman Air da Fly Nas, wadanda sune aka dora wa alhakin wannan aiki a wannan shekarar.

  • Hajji 2022: Jirgi Zai Kwashe Maniyyata 162 Ya Bar 238 A Jihar Edo

Jihar Sakkwato ne a kan gaba na yawan wadanda suka isa kasar mai tsarki da alhazai 1,630, Adamawa nada 1,117; Bauchi 1,303, Benuwai 101; Borno 1,040; Ekiti 136; Abuja 1,535; Gombe 547; Kaduna 793, Katsina 554. Saura sun hada da Kebbi 412; Kogi 361; Kwara 1,100; Lagos 1,598; Ogun 467; Ondo 249; Osun 577; Oyo 340; Yobe 795, Zamfara 1,191, Kano, 339 yayin da zuwa yanzu an yi jigilar jami’an tsaro 329 suwa kasa mai tsarki.

ADVERTISEMENT

Daga cikin Maniyyatar da suka isa kasa mai tsarki ‘yan Nijeriya 12,860 sun dira garin Madinah don gudanar da ibadoji da ziyara yayin da kuma 4,119 suka isa garin Jeddah tun da aka fara jigilar farko a ranar 9 ga watan Yuni daga filin jiragen sama na kasa da kasa da ke Maiduguri babbar birinin Jihar Borno.

Haka kuma bincike ya nuna cewa, bayan Alhazai 11,801 da suka kai ziyara garin Madinah, 5,178 daga cikin su sun riga sun wuce garin Makkah a cigaba da shirye-shiryen ayyukan hajjin bana a kasa mai tsarki.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ganin yadda wa’adin da kasar Saudiya ta gindaya na kwashe maniyyata nata karatowa kuma gashi akwai maniyyata da dama da basu san halin da suke ciki ba, ga kuma wadanda suka biya kudaden su ta kamfanonin jirgin yawo, wanna ya sa hukumar Alhazai NAHCON ta yanke shawarar garzayawa wajen hukumar kasar Saudiya don neman karin kujeru ta yadda dukkan wadanda suka biya kudadensu ta kowacce hanya za su samu sauke farali, hakan ya sa ta tura wata kakkarfar tawaga kasar Saudi Arabiya don nema wa Nijeriya karin kujeru a aikin hajin bana.

Tuni Kwamishina aikin hajji mai kula ayyuka, Abdullahi Hardawa, ya gana da mataimakin Minista mai kula da aikin Hajji da Umara a kan lamarin ranar Lahadi.

A tattaunawarsa da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya, Hardawa ya ce, an mika wa hukumar kasar Saudiyan bukatar kujera 5,000, saboda kanin al’umma sun samu sauke farali a bana.
“Ina Saudiya a halin yanzu ne don neman karin kujeru wanda muka tura bukatar haka tun kafin a fara harkokin aikin hajjin bana.

“Daga sauka ta Riyadh na wuce don ganawa da Ambasadan mu wanda ya bayyana mani irin kokarin da ya ke yi a kan lamarin.

“Sun tabbatar mani da cewa, za su amince da bukatarmu tunda mun riga mun rubuta musu, sun yi alkawarin biya mana bukata.

“Muna bukatar wadannan kujerun ne domin kamfanoni masu jigilar alhazai da kuma maniyyata a jihohi da kuma na bangaren gwamnatin tarayya.

“Bamu taba tunanin za a nemi karin kujerun hajji ba saboda yadda aka kara kudin zuwa hajjin a bana,” in ji shi.
Ya kuma kara da cewa, ya kawo ziyarar zuwa kasa mai tsarki don a kara karfafa bukatar samun kujerun aikin hajjin don al’umma da dama su samu zuwa sauke faralin.

Sai dai a ranar Talata 28 ga watan Yuni 2022 NAHCON ta sanar da cewa, bata samu nasarar neman karin kujerar da suka yi ba, kuma daga yanzu hukumar Saudiyya ta haramtawa duk wanda ya kai shekara 65 kasancewa a cikin masu taimaka wa Alhazai.

Ta bayyana cewa, duk kokarin da hukumar ta yi na samun karin kujerun ya ci tura. Kujeru 43,000 ne aka ba Nijeriya inda aka raba a tsakanin jihohi 36 da Abuja da kuma rundunar sojojin Nijeriya da wasu kamfanonin jigilar alhazai masu zaman kansu.

Amma saboda rikicin da aka samu a tsakanin NAHCON da wasu kamfanonin jigilar na yadda suka yi korafin kujerin da aka basu bai ishesu ba ya sa NAHCON ta garzaya Saudiya don neman karin kujerun don a warware matsalar amma sai gashi hukumar Saudiyya ta ki amincewa da wanna bukatar.
Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara ta bayyana haka a sanawar da ta sanya wa hannu a ranar Talata a Abuja.

•Wasu Ka’doji Sun Canza A Bana
Shugaban Kanfanin zirga-zirgar Alhazai ta ‘Comerel Trabels and Tours Limited’, Ustaz Abubakr Siddeek Muhammad, ya nemi ‘yan Nijeriya masu tafiya sauke farali a bana dasu yi hattara don akwai wasu sabbin dokoki da ka’idoji da kasar Saudiya da aka gindaya wajen ayyukan Haji a bana musamman ganin tasirin annobar cutar Korona da aka fuskanta a shekarar bara.

Ya bayyana haka ne a jawabin da ya yi a taron fadakar da Maniyyata da aka yi a Abuja a makon daya wuce, a wanna shekara gwamnatin kasar Saudiyya ta sanya ido a kan dukkan harkokin da suka shafi ayyukan hajji, ta yadda in banda abin da ya shafi ayyuka na ibada duk an canza dokokin da ke tattare da su. Ya ce, an yi wannan ne do a kara ingata harkokin ayyykan hajji da kara jin dadin Alhazai.

Idab za a iya tunawa an dakatar da baki masu zuwa aikin haji daga kasashe duniya a shekarar 2019, 2020 da kuma 2021 saboda annobar cutar Korona da duniya ta fuskanta.

Wannan ne ya sa hukumar kasa Saudi Arabia ta kayyade masu zuwa hajji a shekarar zuwa mutum 1,000 ‘yan asalin kasar da kuma mutum 10,000 daga wasu kasashe da suka zaba a shekarar 2021.
“An canza abubuwa da dama a cikin shekara uku da suka wuce, sun kuma hada da ayyukan Muassassah wadanda a da suka aiki tare da hukumomin alhazai na jihohi, inda suke samar da musu ayyukan kula da jin dadin alhazai da sauransu.

“A halin yanzu ana gudanar da ayyukan ne daga kwamiti na tsakiya inda daga nan ne za a rinka bayar da odar yadda za a gabatar da aikin wannan kuma wani sabon abune ga masu tafiyar da aikin haji da ma alhazan gaba daya. Saboda haka yakamata kowa ya fahimci wannan dokokin a kamu karbe su a mastayin ayyukan ibada,” inji Ustaz Abubakr.

Ya kuma ce a da ana samun tanti mai lamba ‘tent A’ dadai sauransu amma a wannan shekarar an samar da ‘tent A’ da ‘tent D’ kawai don amfanin Alhazai.

Ya kuma yaba wa Shugaban Hukumar Alhazai (NAHCON) Alhaji Zikrullah Kunle Hassana kokarinsa na tabbatar da an samu nasarar aikin Hajj a wannan shekarar, ya kuma nemi hukumar ta tabbatar da jajircewarta wajen jin dadin alhazai kamar yadda ta saba.

NAHCON
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
NDLEA Ta Damke Mutum 345 Bisa Safarar Kwayoyi A Jihar Katsina

NDLEA Ta Damke Mutum 345 Bisa Safarar Kwayoyi A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.