Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sakon jaje ga shugaban kasar Mozambique Filipe Jacinto Nyusi, sakamakon mahaukaciyar guguwar Chido da ta aukawa kasar.
Cikin sakon da ya aike a jiya, shugaba Xi ya bayyana cewa, ya samu labarin cewa, mutane da dama sun mutu, wasu kuma sun jikkata, kuma an samu hasara da dama sakamakon ibtila’in. Ya ce a madadin gwamnati da jama’ar kasar Sin, yana jajantawa mutane da iyalan wadanda ibtila’in ya rutsa da su. Ya ce, a wannan lokaci, jama’ar kasar Sin da jama’ar Mozambique suna tare da juna, kuma Sin tana son bayar da gudummawa ga Mozambique wajen sake gina kasar bayan ibtila’in. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp