• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Shugaban Rikon Kwarya Na Gabon Game Da Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Jakadanci Tsakanin Sassan Biyu

by Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Shugaban Rikon Kwarya Na Gabon Game Da Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Jakadanci Tsakanin Sassan Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Asabar, 20 ga watan nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi musayar sakon taya murna da shugaban rikon kwarya na kasar Gabon Brice Clotaire Oligui Nguema, game da cika shekaru 50 da kulla huldar jakadanci tsakanin kasashen biyu.

A cikin sakon, shugaba Xi ya nuna cewa, a cikin rabin karnin da ya gabata, duk da yadda yanayin da ake ciki a duniya ke ci gaba da canjawa, kasashen Sin da Gabon sun ci gaba da daukar juna daidai, kana suna goyon bayan juna, yayin da dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu ke kara ingantuwa, wanda hakan ya haifar da fa’ida ta gaske ga jama’ar kasashen biyu.

  • NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2
  • Wani Mutum Ya Mutu Bayan Ya Cinna Wa Kansa Wuta A Yayin Da Ake Shari’ar Trump

Xi Jinping ya kara da cewa, yana mayar da hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Gabon, kuma yana son yin aiki tare da shugaba Nguema, don daukar bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu a matsayin wani sabon mafari, na ci gaba da sada zumuncin gargajiya tsakanin kasashen biyu, da zurfafa hakikanin hadin gwiwa, da wadatar da abubuwan da suka shafi dangantakar abokantaka, ta hadin kai bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, da kuma hada gwiwa don gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga Sin da kasashen Afirka.

A nasa bangaren, shugaba Nguema ya bayyana cewa, kasarsa na tsayawa kan bin manufar Sin daya tak, kuma ta yi imanin cewa, Taiwan wani bangare ne na kasar Sin da ba za a iya balle shi ba. Ya ce kasar Gabon tana son yin aiki tare da kasar Sin, wajen ciyar da dangantakar abokantaka ta hadin kai bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni tsakanin kasashen biyu gaba, tare da amfanar da jama’ar kasashen biyu.

A wannan rana kuma, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, da takwaransa na kasar Gabon Ali Akbar Onanga Y’obeghe, sun aike da sako ga juna, don taya murnar cika shekaru 50 da kulla huldar jakadanci tsakanin kasashen biyu. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burina Na Yi Rubutun Da Ko Ba Ni A Yi Alfahari Da Shi Ba Na Allah Wadai Ba – Mustapha

Next Post

Kasar Amurka Na Illata Al’amuran Kasa Da Kasa Da Na Shiyya-Shiyya

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

4 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

20 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
Kasar Amurka Na Illata Al’amuran Kasa Da Kasa Da Na Shiyya-Shiyya

Kasar Amurka Na Illata Al’amuran Kasa Da Kasa Da Na Shiyya-Shiyya

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Xi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.