Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta sanar da cewa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci bikin bude taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa Sin da Afirka, wato FOCAC na shekarar 2024 tare da gabatar da jawabi a ran 5 ga watan Satumba mai zuwa. Yayin taron, Xi Jinping zai shirya liyafa don tarban shugabannin kasashen Afirka da wakilan kungiyoyin yankin Afirka da na duniya wadanda za su halarci taron da sauran ayyuka. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp