• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaƙi Da ‘Yan Bindiga: Yadda Gwamna Dauda Ya Karɓi Baƙuncin Babban Hafsan Tsaro

by Leadership Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Yaƙi Da ‘Yan Bindiga: Yadda Gwamna Dauda Ya Karɓi Baƙuncin Babban Hafsan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar wa rundunar sojojin ƙasar nan jajircewar gwamnatinsa wajen bai wa jami’an soji cikakken goyon bayan gwamnatin sa a jihar Zamfara. 

 

Ranar Juma’ar da ta gabata, Gwamna Lawal ya karɓi baƙuncin Babban Hafsan tsaron ƙasa (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa a tsohon ɗakin taron fadar gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 40 A Hatsarin Kwale-kwale
  • Bukukuwan Mauludi: Wani Mummunan Hatsari Ya Ci Rayukan Mutane 40 A Saminaka

Sanarwa daga mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ta bayyana cewa Babban Hafsan tsaron ya sanar da wani laƙabi da za a rinƙa kiran rundunar haɗin gwiwa ta yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma, inda ya ce za a rinƙa kiranta da ‘rundunar samamen Fansan Yamma, wanda kuma yanzu ita ce rundunar da aka sani a yankin Arewa maso Yamma.

 

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan runduna ta ‘Operation Fansan Yamma,’ wani laƙabi ne da ke nuni da cewa jami’an tsaron a shirye su ke don ganin sun murƙushe harkar ‘yan bindiga a yankin na Arewa maso Yamma.

 

Cikin jawabin sa, Gwamna Dauda ya yaba wa Babban Hafsan bisa irin namijin ƙoƙarin da ya ke yi wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan.

Bindiga

“Janar, kasancewarka a Zamfara a wannan lokaci, ya ƙara ƙara wa jami’an soji ƙwarin gwiwa. Ka ƙara tabbatar da fatan mu, al’umma na cike da fata.

 

“Ba za mu taɓa yin wasa da wannan ziyara ba. Gwamnatina ta jajirce wajen haɗa kai da Hukumomin tsaro don tabbatar da tsaro a jihar Zamfara.

 

“Bisa la’akari da jawabinka, ina da tabbacin cewa zaman lafiya zai dawo a Zamfara. Ka yi makaranta a nan, ka san irin yanayin zaman lafiyar da ake da shi a da. Gusau ta kasance birni na biyu a harkar Kasuwanci a Arewa bayan jihar Kano.

 

“Na ji daɗin kasacewa kana aiki tare da rundunar Askarawan Zamfara ta CPG. Ina so ka sani, kafin a zaɓi Askarawan Zamfara sai da Hukumar tsaro ta DSS da sauran hukumomin tsaro suka tantance su.

 

“Muna bayar da cikakken goyon bayan mu ga sojoji a ƙoƙarin su na yaƙi da ‘yan bindiga. An tura waɗannan jami’ai zuwa yankunan su. Muna da yaƙinin cewa sojoji a jajirce suke wajen magance matsalar tsaro.

 

“Zan yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta’aziyyata bisa jajirtattun jami’an da suka rasu a hanyar Gusau zuwa Funtuwa. Allah gafarta masu. Ina tabbatar maka da cewa gwamnatina na tare da kai, kuma za mu ci gaba da aiki tare da jami’an soji da sauran hukumomin tsaro don kawo ƙarshen ‘yan bindiga.”

Bindiga

Tun farko a jawabinsa, Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, ya nuna matuƙar godiyar sa ga Gwamna Dauda Lawal bisa goyon bayan da ya ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro a jihar. “Mun zo nan ne don muna godiyar mu bisa irin goyon bayan da ka ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro, tare da irin gagarumar ci gaban da kake samarwa a jihar Zamfara.

 

“Na kasance ina alfahari da Gusau da na sani, amma gaskiya, yanzu abin da na gani, sai na rasa me zan ce. Yabon gwani ya zama dole bisa irin ci gaban da ka samar wa Zamfara a shekara ɗaya kacal, a ƙarƙashin jagorancinka. Ina gode maka bisa inganta rayuwar al’umma. Wannan romon Dimokraɗiyya ne. Muna ganin ci gaba da dama, tare da wasu ayyukan da ake gudanarwa a jihar, tun bayan hawan ka mulki.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BaleriYaki da Yan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Next Post

WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

12 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

24 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

LABARAI MASU NASABA

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.