ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaƙi Da ‘Yan Bindiga: Yadda Gwamna Dauda Ya Karɓi Baƙuncin Babban Hafsan Tsaro

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Bindiga

Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar wa rundunar sojojin ƙasar nan jajircewar gwamnatinsa wajen bai wa jami’an soji cikakken goyon bayan gwamnatin sa a jihar Zamfara. 

 

Ranar Juma’ar da ta gabata, Gwamna Lawal ya karɓi baƙuncin Babban Hafsan tsaron ƙasa (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa a tsohon ɗakin taron fadar gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 40 A Hatsarin Kwale-kwale
  • Bukukuwan Mauludi: Wani Mummunan Hatsari Ya Ci Rayukan Mutane 40 A Saminaka

Sanarwa daga mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ta bayyana cewa Babban Hafsan tsaron ya sanar da wani laƙabi da za a rinƙa kiran rundunar haɗin gwiwa ta yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma, inda ya ce za a rinƙa kiranta da ‘rundunar samamen Fansan Yamma, wanda kuma yanzu ita ce rundunar da aka sani a yankin Arewa maso Yamma.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan runduna ta ‘Operation Fansan Yamma,’ wani laƙabi ne da ke nuni da cewa jami’an tsaron a shirye su ke don ganin sun murƙushe harkar ‘yan bindiga a yankin na Arewa maso Yamma.

 

Cikin jawabin sa, Gwamna Dauda ya yaba wa Babban Hafsan bisa irin namijin ƙoƙarin da ya ke yi wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan.

Bindiga

“Janar, kasancewarka a Zamfara a wannan lokaci, ya ƙara ƙara wa jami’an soji ƙwarin gwiwa. Ka ƙara tabbatar da fatan mu, al’umma na cike da fata.

 

“Ba za mu taɓa yin wasa da wannan ziyara ba. Gwamnatina ta jajirce wajen haɗa kai da Hukumomin tsaro don tabbatar da tsaro a jihar Zamfara.

 

“Bisa la’akari da jawabinka, ina da tabbacin cewa zaman lafiya zai dawo a Zamfara. Ka yi makaranta a nan, ka san irin yanayin zaman lafiyar da ake da shi a da. Gusau ta kasance birni na biyu a harkar Kasuwanci a Arewa bayan jihar Kano.

 

“Na ji daɗin kasacewa kana aiki tare da rundunar Askarawan Zamfara ta CPG. Ina so ka sani, kafin a zaɓi Askarawan Zamfara sai da Hukumar tsaro ta DSS da sauran hukumomin tsaro suka tantance su.

 

“Muna bayar da cikakken goyon bayan mu ga sojoji a ƙoƙarin su na yaƙi da ‘yan bindiga. An tura waɗannan jami’ai zuwa yankunan su. Muna da yaƙinin cewa sojoji a jajirce suke wajen magance matsalar tsaro.

 

“Zan yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta’aziyyata bisa jajirtattun jami’an da suka rasu a hanyar Gusau zuwa Funtuwa. Allah gafarta masu. Ina tabbatar maka da cewa gwamnatina na tare da kai, kuma za mu ci gaba da aiki tare da jami’an soji da sauran hukumomin tsaro don kawo ƙarshen ‘yan bindiga.”

Bindiga

Tun farko a jawabinsa, Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, ya nuna matuƙar godiyar sa ga Gwamna Dauda Lawal bisa goyon bayan da ya ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro a jihar. “Mun zo nan ne don muna godiyar mu bisa irin goyon bayan da ka ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro, tare da irin gagarumar ci gaban da kake samarwa a jihar Zamfara.

 

“Na kasance ina alfahari da Gusau da na sani, amma gaskiya, yanzu abin da na gani, sai na rasa me zan ce. Yabon gwani ya zama dole bisa irin ci gaban da ka samar wa Zamfara a shekara ɗaya kacal, a ƙarƙashin jagorancinka. Ina gode maka bisa inganta rayuwar al’umma. Wannan romon Dimokraɗiyya ne. Muna ganin ci gaba da dama, tare da wasu ayyukan da ake gudanarwa a jihar, tun bayan hawan ka mulki.”

Bindiga
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
Bindiga
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.