• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Binciki Bankin Raya Kasa Da Gwamnati Ta Kafa – Ndume

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
Ya Kamata A Binciki Bankin Raya Kasa Da Gwamnati Ta Kafa – Ndume
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kwamitin Rundunar Soji a Majalisar Dattawa, Sanata Muhammad Ndume ya bayyana cewa akwai bukatar a binciki Bankin Ci Gaban Nijeriya watau Development Bank of Nigeria (DBN) da Gwamnatin Tarayya ta kafa domin taimakawa kananan masana’antu da `yan Kasuwa sakamakon zargin gudanar da al’amura ta hanyar da bata dace ba.

  • Buhari Ya Halarci Wajen Kaddamar Da Hako Man Fetur A Bauchi 

Ndume wanda ya kasance mamba a cikin wani kwamitin na wucin gadi na mutane bakwai da Sanata Muhammad Sani Musa 313 ke jagoranta a Majalisar Dattawan Tarayyar, ya yi nuni da cewa a wani binciken da suka yi alamu na nuni da cewa kwalliya ba ta biya kuɗin sabulu ba.

Ya kara da cewa an kawo Kudirin Dokar ne domin a binciki Bankin ta DBN wanda Gwamnatin Tarayya ta kafa saboda tabbatar da an taimaka wa kananan `yan Kasuwa da masana’antu domin su samu tallafi mai sauki ta yadda za su farfado ko su kafa kananan masana’antu wanda yake da mahimmaci ga masu kananan karfi domin idan aka farfado da wannan `yan Kasuwa da masana’antu shi ne za a iya farfado da tattalin Arzikin Kasar.

Ya ce “amma abun takaici shi ne mun lura a cikin wani bincike cewa Bankin DBN a cikin shekarar 2021, ta rabar da kudi kusan kimanin rabin Tiriliyan, amma abun takaici shi ne inda talauci ya fi katutu kuma inda ake bukatar a farfado da kananan masana’antu ba su samu ko rabin abin da suka rabar ba.

“Na gano cewa Jihar Legas kadai a cikin Kudi naira Biliyan 483 sun samu kashi 47% amma sauran shiyyar Kudu maso yamma sun samu kashi 10 wanda gaba daya kudin ya kama naira Tiriliyan 274 a yayin da daga cikin Jihohi shida na Kudu maso yamma, ita Jihar Legas kadai ke da Kudi kimanin naira Biliyan 227 amma sauran Jihohin biyar ke da kashi 10.

Labarai Masu Nasaba

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

“Haka Kudu maso Kudu sun samu kashi 17 da ya kama Naira Biliyan 81, amma gaba dayan Arewa da ke da Jahohi 19 sun samu kashi 11 wanda ya kama kimanin naira Biliyan 53, domin a shiyyar Arewa maso gabas ta samu kashi 5 wato naira Biliyan 24, sai shiyyar Arewa maso yamma ta samu kashi daya wato Naira Biliyan 4,820.

 

“Makasudin kafa wannan Bankin shi ne don ta taimaka wa kananan `yan Kasuwa da masana’antu wanda sune ke fannin Noma, kasuwanci, sufuri amma sai muka ga sun dauki kashi 42 na kudin sun ba masu harkar mai.

 

“Kudin da aka bayar ga shiyyoyin 6 bashi ne ake bayarwa mai sassauci don farfado da tattalin Arzikin Kasa ta hanyar Bankin don ita Bankin da za ta bayar, ba tana bayarwa ba ne don riba sai don a taimaka.

“Misali a Jihar Kano da Sokoto an rufe masana’antu da yawa don ba Kudin da za a farfado da su, shi ne ya sa ake so a basu wannan kudin da zai zamanto ba za a kuntata musu ba, toh amma kwalliya ba ta biya kuɗin sabulu ba.

Acewarsa, akwai bukatar a yi bincike don sanin shin nawa ne Kudin, mai yasa aka rabar da kudin haka, meye za ayi don tabbatar cewa dalilin da ya sa aka kafa wannan Banki da kuma tabbatar da cewa Kudaden da ake rabar sun je ga hannun wadanda ya kamata, kuma `yan Nijeriya su gani a kasa ta hanyar tabbatar da cewa kananan masana’antu na tasowa ta hanyar taimakon wannan Banki tunda a bisa wannan dalilin ya sa aka kafa Bankin na DBN.

“Kuma akwai Bankin Kasuwanci (BOI), NIRSAL ta CBN da Gwamnatin Tarayya da suka sha fitar da wadansu hanyoyin da tsari don taimaka wa `yan Nijeriya talakawa amma har yanzu ba a gani a Kasa ba saboda matsalar wadanda aka saka su su yi aikin ya sa muke son mu yi bincike a Majalisar domin idan da akwai wadanda suka hana ruwa gudu, sai a san yadda za a yi a kawar da su domin a samu tsari mai kyau a kan abin da ake bukata.

“An hada kwamitin wucin Gadi na mutum bakwai, an saka ni member kuma Inshaa Allah za mu tabbatar da cewa an yi abun da ya dace don tabbatar da cewa `yan Nijeriya sun ga abin da aka yi tare da tabbatar cewa an yi maganin matsalar.

“A yanzu talauci ya addabi `yan Nijeriya musamman Arewa. A kiyasi, Jihar Kebbi na fama da talauci kimanin kashi 86, Jihar Gombe 77, Jihar Bauchi 87, Jihar Taraba 78, Jihar Zamfara kashi 80, sannan kusan rabin Jihar Filato na fama da talauci, haka sama da rabin `yan Jihar Ebonyi su ma suna fama da talauci, shi yasa ni a matsayin wakili na kai wannan lamarin gaban Majalisar don a yi wa tubkar hanci, a yi maganin lamarin kuma `yan uwana `yan majalisar sun karbi abun hannu biyu-biyu, don haka suka bani goyon baya.” Inji Ndume


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Ganawa Tsakanin Ministocin Tsaron Kasashen Sin Da Amurka 

Next Post

Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

Related

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

2 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

2 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

2 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

5 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

7 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

22 hours ago
Next Post
Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.