• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayoyi
0
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alhaji Abdullahi Yaluwa Ajiyan Yawuri, shi ne shugaban ‘yan Arewa masu mallakar gidajen Rediyo da Talabijin. A tattauanwar da ya yi da wakilinmu, ya bayyana matsayar kungiyarsu a kan yadda aka wulakanta yara kanana da sunan gurfanar da su a kan shiga zanga-zangar tsadar rayuwa watanni 6 da suka wuce. Ga dai bayanan da ya yi.

 

“Makasudin wannan labari da muka fitar shi ne bayan mun ga hotuna a Soshiyal Midiya da yara kanana, duk wanda ya dube su za ka ga tsoro da barazana a fuskokinsu, da yunwa da kuma shida ta cewa an tirsasa musu da wuya, an kuma yi amfani da tsari na yunwa, kuma babban abin tambaya ma yanzu shi ne, su wadannan da Allah ya sa aka gani kila su Allah ya yi musu gyadar dogo, to me ya samu sauran da kila Allah bai nufa su an kawo su kotun ba?

  • NAHCON Za Ta Biya Alhazai Diyyar Wasu Kuɗaɗe Kan Ƙarancin Kula Da Su Lokacin Hajji
  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

“To babu shakka wannan tsari na shugabancin rashin gaskiya da muka gani dole ya tayar wa kowa hankali ba a Arewa kawai ba a duk duniya, kuma ya nuna cewa a karkashin wannan shugabanci na Bola Ahmed Tinibu Nijeriya fa ta kama hanyar lalacewa, kuma babu yadda za a yi mu kira kanmu da kasa mai aiki da Dimukradiyya.

 

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

“To wadannan yara an zarge su ne wasu daga cikinsu dai yan shekaru 12 wasu 13 wasu 14, an zarge su wai da yi wa Nijeriya zagon kasa, to ka dubi wadannan yaran ka ce wai su ne su kai barazanar tunbuke gwamnatin Tinubu, to ka san babau shakka akwai rashin hankali a wannan zaton.

 

‘’Kuma abin da yake bani mamaki shi ne, gwanati da ta ce tana da masaniya akan mutanen da suka assasa wannan zanga-zangar ta #EndBadGobernace# har yanzu ba a kawo su kotu ba sai wadannan yara wanda yawancin su ma idan a wajen zanga-zangar aka kama su, to sun tafi tafi ne kawai a matsayin yaro ya ji abin hanyaniya ya ruga ya gani kuma wannan a gidan kowa akwai irin su.

 

Mun yi kira ga gwamnati da ta saki wadannan yaran kuma ta tabbatar da an kiyaye lafiyarsu, kuma wadanda ba su da kafiya muna kira ga gwamnati ta fita da su kasar waje kamar yadda shugaban kasa ke fita a kai su Faransa a kai su Ingila domin a duba lafiyarsu, kuma a biya su diyya, sannan duk wani wanda ke da hannu a cikin wannan ta’asar daga Babban Sufeto Janar na ‘Yansanda zuwa mai shari’a, lauyoyin gwamnati ma, to duk wanda ke hannu a wannan Fir’aunancin, muna kira ga gwamnati ta kama su a yi wani kwamiti da za ta bicike su kuma wanda aka kama da laifi a horar da shi. mun jaddada wa gwamnati cewa, matsaloli da Nijeriya ke ciki ba ‘yan Nijeriya suka jawo shi ba, tsarin shugabancin wannan gwamnatin ne ya kawo wadannan matsaloli, kuma ‘yan Nijerita ba za su daina fitowa zanga-zanga ba domin wadanda ke shugabancin mu yanzu ba su fi mu zama ‘yan Nijeriya ba.

 

“Bayan haka, muna neman cewa tsare-tsare na gwamnati dake kawo mana bala’i, da jawo mana fakirci, dake sa mutane suna mutuwa a gidansu da yunwa, to muna kira ga gwamnati ta janye wadannan.

 

“Maganar tallafi akan fetur, maganar tallafi akan biyan biyan kudin wuta, maganar tallafi akan sauran abubuwa na gwamnati da wasu kasashe ke yi, ko kasashen da ke amfani da jari hujja ba su daina ba da irin wannnan tallafin ba, muna kira ga gwamnati ta janye wadannan tsare-tsare kuma a dawo mana da tsarin da muka amince domin su ne shugabannin, amma mu ake shigabanta, kuma yadda za a ce ra’ayinmu bai da wani muhimmanci akan yadda gwamnati za ta gudanar da shugabancinta, mun gaji da ba mu hakuri, “Mun gaji da gafara sa muna so mu gani a kasa, ita ce babbar magana kuma shi ne babban kiran da muka yi ga gwamnati”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

Next Post

Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

6 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

12 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

12 months ago
Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

12 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

1 year ago
Yara
Ra'ayoyi

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

1 year ago
Next Post
Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.