• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

byLeadership Hausa and Sulaiman
11 months ago
Yara

Alhaji Abdullahi Yaluwa Ajiyan Yawuri, shi ne shugaban ‘yan Arewa masu mallakar gidajen Rediyo da Talabijin. A tattauanwar da ya yi da wakilinmu, ya bayyana matsayar kungiyarsu a kan yadda aka wulakanta yara kanana da sunan gurfanar da su a kan shiga zanga-zangar tsadar rayuwa watanni 6 da suka wuce. Ga dai bayanan da ya yi.

 

“Makasudin wannan labari da muka fitar shi ne bayan mun ga hotuna a Soshiyal Midiya da yara kanana, duk wanda ya dube su za ka ga tsoro da barazana a fuskokinsu, da yunwa da kuma shida ta cewa an tirsasa musu da wuya, an kuma yi amfani da tsari na yunwa, kuma babban abin tambaya ma yanzu shi ne, su wadannan da Allah ya sa aka gani kila su Allah ya yi musu gyadar dogo, to me ya samu sauran da kila Allah bai nufa su an kawo su kotun ba?

  • NAHCON Za Ta Biya Alhazai Diyyar Wasu Kuɗaɗe Kan Ƙarancin Kula Da Su Lokacin Hajji
  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

“To babu shakka wannan tsari na shugabancin rashin gaskiya da muka gani dole ya tayar wa kowa hankali ba a Arewa kawai ba a duk duniya, kuma ya nuna cewa a karkashin wannan shugabanci na Bola Ahmed Tinibu Nijeriya fa ta kama hanyar lalacewa, kuma babu yadda za a yi mu kira kanmu da kasa mai aiki da Dimukradiyya.

 

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

“To wadannan yara an zarge su ne wasu daga cikinsu dai yan shekaru 12 wasu 13 wasu 14, an zarge su wai da yi wa Nijeriya zagon kasa, to ka dubi wadannan yaran ka ce wai su ne su kai barazanar tunbuke gwamnatin Tinubu, to ka san babau shakka akwai rashin hankali a wannan zaton.

 

‘’Kuma abin da yake bani mamaki shi ne, gwanati da ta ce tana da masaniya akan mutanen da suka assasa wannan zanga-zangar ta #EndBadGobernace# har yanzu ba a kawo su kotu ba sai wadannan yara wanda yawancin su ma idan a wajen zanga-zangar aka kama su, to sun tafi tafi ne kawai a matsayin yaro ya ji abin hanyaniya ya ruga ya gani kuma wannan a gidan kowa akwai irin su.

 

Mun yi kira ga gwamnati da ta saki wadannan yaran kuma ta tabbatar da an kiyaye lafiyarsu, kuma wadanda ba su da kafiya muna kira ga gwamnati ta fita da su kasar waje kamar yadda shugaban kasa ke fita a kai su Faransa a kai su Ingila domin a duba lafiyarsu, kuma a biya su diyya, sannan duk wani wanda ke da hannu a cikin wannan ta’asar daga Babban Sufeto Janar na ‘Yansanda zuwa mai shari’a, lauyoyin gwamnati ma, to duk wanda ke hannu a wannan Fir’aunancin, muna kira ga gwamnati ta kama su a yi wani kwamiti da za ta bicike su kuma wanda aka kama da laifi a horar da shi. mun jaddada wa gwamnati cewa, matsaloli da Nijeriya ke ciki ba ‘yan Nijeriya suka jawo shi ba, tsarin shugabancin wannan gwamnatin ne ya kawo wadannan matsaloli, kuma ‘yan Nijerita ba za su daina fitowa zanga-zanga ba domin wadanda ke shugabancin mu yanzu ba su fi mu zama ‘yan Nijeriya ba.

 

“Bayan haka, muna neman cewa tsare-tsare na gwamnati dake kawo mana bala’i, da jawo mana fakirci, dake sa mutane suna mutuwa a gidansu da yunwa, to muna kira ga gwamnati ta janye wadannan.

 

“Maganar tallafi akan fetur, maganar tallafi akan biyan biyan kudin wuta, maganar tallafi akan sauran abubuwa na gwamnati da wasu kasashe ke yi, ko kasashen da ke amfani da jari hujja ba su daina ba da irin wannnan tallafin ba, muna kira ga gwamnati ta janye wadannan tsare-tsare kuma a dawo mana da tsarin da muka amince domin su ne shugabannin, amma mu ake shigabanta, kuma yadda za a ce ra’ayinmu bai da wani muhimmanci akan yadda gwamnati za ta gudanar da shugabancinta, mun gaji da ba mu hakuri, “Mun gaji da gafara sa muna so mu gani a kasa, ita ce babbar magana kuma shi ne babban kiran da muka yi ga gwamnati”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

October 4, 2024
Next Post
Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version