• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Yi Karin Haske Kan Fashewar Bututun Nord Stream

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Fashewar bututun iskar gas na Nord Stream da ya auku a watan Satumban bara, ya sake jawo hankalin duniya a kwanakin baya, sakamakon yadda shahararren dan jaridan Amurka, Seymour Hersh ya ruwaito cewa, gwamnatin Biden ce ta tsara shirin lalata bututun wanda kasar Rasha ke amfani da shi don jigilar iskar gas dinta zuwa kasashen Turai.

Duk da cewa kwamitin tsaron kasa na fadar White House, da hukumar tattara bayanan sirri ta Amurka wato CIA, da ma’aikatar harkokin wajen kasar, da ma sauran sassan gwamnatin Amurka duk sun musanta rahoton, amma bisa yin la’akari da sunan Seymour Hersh a fagen watsa labarai na Amurka, da ma cikakkun bayanai da aka rubuta filla filla game da lamarin, ana ganin cewa, ruwa ba ya tsami a banza.

Ko mene ne gaskiyar lamarin? Ya zama dole a kara yin bincike don tabbatar da amsa. Amma wani abin da muke iya tabbatarwa shi ne Amurka ce ta fi amfana da lamarin fashewar bututun, kasancewar bututun ya dade yana damun kasar Amurka, musamman ma bayan aukuwar rikici a tsakanin Rasha da Ukraine, ’yan siyasar Amurka sun san cewa, muddin dai bututun yana nan, ba zai yiwu kasashen Turai da Rasha su bata kwata kwata ba. Kaza lika abun da ya faru, ya tabbatar da cewa, kawo yanzu ba kawai Amurka ta cimma moriyar siyasa daga rikicin Rasha da Ukraine ba ne, har ma ta samu muguwar riba daga isar gas da ta sayar wa kasashen Turai a kan farashi mai tsada.

Idan ba a manta ba, a makwanni kafin aukuwar rikicin, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi gargadin cewa, idan dai Rasha ta kaddamar da yaki a kan kasar Ukraine, “za mu kawo karshen Nord Stream-2”, bayan da bututun ya fashe kuma, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya bayyana cewa, “ya zama babbar nasara a karshe”, wanda zai taimaka wa Turai wajen “daina dogaro ga Rasha ta fannin makamashi”. To, sai yanzu ne muka gane abin da suke nufi.

Bututun iskar gas na Nord Stream, muhimmin aikin more rayuwa ne da aka gina tsakanin kasa da kasa. Kuma lalacewarsu ya haifar da mummunar illa ga kasuwar makamashi, gami da muhallin halittun duniya, don haka dole a hukunta wadanda suka aikata laifin lalata shi.

LABARAI MASU NASABA

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Idan an tabbatar da gaskiyar rahoton binciken da dan jaridan Amurka Hersh ya wallafa, to, lamarin ya zama aikin ta’addanci da wata kasa ta aikata ke nan, wanda sam ba za a iya amincewa da shi ba. Haka kuma, ya zama dole Amurka ta maida martani game da shakkun da kasa da kasa ke nunawa a kan ta, da bada hadin-kai don binciken musababbin aukuwar lamarin, saboda duniya na bukatar adalci da sanin gaskiya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta
Daga Birnin Sin

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni
Daga Birnin Sin

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Next Post
Sin: Sake Bude Hada-hadar Yawon Shakatawa Za Ta Kara Zurfafa Musayar Sin Da Sauran Sassan Duniya

Sin: Sake Bude Hada-hadar Yawon Shakatawa Za Ta Kara Zurfafa Musayar Sin Da Sauran Sassan Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Amurka

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.