• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Yi Karin Haske Kan Fashewar Bututun Nord Stream

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Amurka Ta Yi Karin Haske Kan Fashewar Bututun Nord Stream
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fashewar bututun iskar gas na Nord Stream da ya auku a watan Satumban bara, ya sake jawo hankalin duniya a kwanakin baya, sakamakon yadda shahararren dan jaridan Amurka, Seymour Hersh ya ruwaito cewa, gwamnatin Biden ce ta tsara shirin lalata bututun wanda kasar Rasha ke amfani da shi don jigilar iskar gas dinta zuwa kasashen Turai.

Duk da cewa kwamitin tsaron kasa na fadar White House, da hukumar tattara bayanan sirri ta Amurka wato CIA, da ma’aikatar harkokin wajen kasar, da ma sauran sassan gwamnatin Amurka duk sun musanta rahoton, amma bisa yin la’akari da sunan Seymour Hersh a fagen watsa labarai na Amurka, da ma cikakkun bayanai da aka rubuta filla filla game da lamarin, ana ganin cewa, ruwa ba ya tsami a banza.

Ko mene ne gaskiyar lamarin? Ya zama dole a kara yin bincike don tabbatar da amsa. Amma wani abin da muke iya tabbatarwa shi ne Amurka ce ta fi amfana da lamarin fashewar bututun, kasancewar bututun ya dade yana damun kasar Amurka, musamman ma bayan aukuwar rikici a tsakanin Rasha da Ukraine, ’yan siyasar Amurka sun san cewa, muddin dai bututun yana nan, ba zai yiwu kasashen Turai da Rasha su bata kwata kwata ba. Kaza lika abun da ya faru, ya tabbatar da cewa, kawo yanzu ba kawai Amurka ta cimma moriyar siyasa daga rikicin Rasha da Ukraine ba ne, har ma ta samu muguwar riba daga isar gas da ta sayar wa kasashen Turai a kan farashi mai tsada.

Idan ba a manta ba, a makwanni kafin aukuwar rikicin, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi gargadin cewa, idan dai Rasha ta kaddamar da yaki a kan kasar Ukraine, “za mu kawo karshen Nord Stream-2”, bayan da bututun ya fashe kuma, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya bayyana cewa, “ya zama babbar nasara a karshe”, wanda zai taimaka wa Turai wajen “daina dogaro ga Rasha ta fannin makamashi”. To, sai yanzu ne muka gane abin da suke nufi.

Bututun iskar gas na Nord Stream, muhimmin aikin more rayuwa ne da aka gina tsakanin kasa da kasa. Kuma lalacewarsu ya haifar da mummunar illa ga kasuwar makamashi, gami da muhallin halittun duniya, don haka dole a hukunta wadanda suka aikata laifin lalata shi.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Idan an tabbatar da gaskiyar rahoton binciken da dan jaridan Amurka Hersh ya wallafa, to, lamarin ya zama aikin ta’addanci da wata kasa ta aikata ke nan, wanda sam ba za a iya amincewa da shi ba. Haka kuma, ya zama dole Amurka ta maida martani game da shakkun da kasa da kasa ke nunawa a kan ta, da bada hadin-kai don binciken musababbin aukuwar lamarin, saboda duniya na bukatar adalci da sanin gaskiya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-Zangar Sauya Kudi: Gwamnan Kwara Ya Dakatar Da Taron Yakin Neman Zabe A Jihar

Next Post

Sin: Sake Bude Hada-hadar Yawon Shakatawa Za Ta Kara Zurfafa Musayar Sin Da Sauran Sassan Duniya

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

13 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

15 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

16 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

17 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
Sin: Sake Bude Hada-hadar Yawon Shakatawa Za Ta Kara Zurfafa Musayar Sin Da Sauran Sassan Duniya

Sin: Sake Bude Hada-hadar Yawon Shakatawa Za Ta Kara Zurfafa Musayar Sin Da Sauran Sassan Duniya

LABARAI MASU NASABA

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.