ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Yi Karin Haske Kan Fashewar Bututun Nord Stream

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Fashewar bututun iskar gas na Nord Stream da ya auku a watan Satumban bara, ya sake jawo hankalin duniya a kwanakin baya, sakamakon yadda shahararren dan jaridan Amurka, Seymour Hersh ya ruwaito cewa, gwamnatin Biden ce ta tsara shirin lalata bututun wanda kasar Rasha ke amfani da shi don jigilar iskar gas dinta zuwa kasashen Turai.

Duk da cewa kwamitin tsaron kasa na fadar White House, da hukumar tattara bayanan sirri ta Amurka wato CIA, da ma’aikatar harkokin wajen kasar, da ma sauran sassan gwamnatin Amurka duk sun musanta rahoton, amma bisa yin la’akari da sunan Seymour Hersh a fagen watsa labarai na Amurka, da ma cikakkun bayanai da aka rubuta filla filla game da lamarin, ana ganin cewa, ruwa ba ya tsami a banza.

Ko mene ne gaskiyar lamarin? Ya zama dole a kara yin bincike don tabbatar da amsa. Amma wani abin da muke iya tabbatarwa shi ne Amurka ce ta fi amfana da lamarin fashewar bututun, kasancewar bututun ya dade yana damun kasar Amurka, musamman ma bayan aukuwar rikici a tsakanin Rasha da Ukraine, ’yan siyasar Amurka sun san cewa, muddin dai bututun yana nan, ba zai yiwu kasashen Turai da Rasha su bata kwata kwata ba. Kaza lika abun da ya faru, ya tabbatar da cewa, kawo yanzu ba kawai Amurka ta cimma moriyar siyasa daga rikicin Rasha da Ukraine ba ne, har ma ta samu muguwar riba daga isar gas da ta sayar wa kasashen Turai a kan farashi mai tsada.

ADVERTISEMENT

Idan ba a manta ba, a makwanni kafin aukuwar rikicin, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi gargadin cewa, idan dai Rasha ta kaddamar da yaki a kan kasar Ukraine, “za mu kawo karshen Nord Stream-2”, bayan da bututun ya fashe kuma, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya bayyana cewa, “ya zama babbar nasara a karshe”, wanda zai taimaka wa Turai wajen “daina dogaro ga Rasha ta fannin makamashi”. To, sai yanzu ne muka gane abin da suke nufi.

Bututun iskar gas na Nord Stream, muhimmin aikin more rayuwa ne da aka gina tsakanin kasa da kasa. Kuma lalacewarsu ya haifar da mummunar illa ga kasuwar makamashi, gami da muhallin halittun duniya, don haka dole a hukunta wadanda suka aikata laifin lalata shi.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Idan an tabbatar da gaskiyar rahoton binciken da dan jaridan Amurka Hersh ya wallafa, to, lamarin ya zama aikin ta’addanci da wata kasa ta aikata ke nan, wanda sam ba za a iya amincewa da shi ba. Haka kuma, ya zama dole Amurka ta maida martani game da shakkun da kasa da kasa ke nunawa a kan ta, da bada hadin-kai don binciken musababbin aukuwar lamarin, saboda duniya na bukatar adalci da sanin gaskiya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Sin: Sake Bude Hada-hadar Yawon Shakatawa Za Ta Kara Zurfafa Musayar Sin Da Sauran Sassan Duniya

Sin: Sake Bude Hada-hadar Yawon Shakatawa Za Ta Kara Zurfafa Musayar Sin Da Sauran Sassan Duniya

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.