• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Girmama Alkawarin Da Ta Dauka Game Da Batun Tsibiran Malvinas

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Birtaniya Ta Girmama Alkawarin Da Ta Dauka Game Da Batun Tsibiran Malvinas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, ofishin jakadancin Birtaniya dake Argentina, ya gabatar da wata gasar bidiyo a kan yanar gizo, ga daliban jami’o’in dake kasar, inda ofishin ya yi ikirarin cewa, wanda ya lashe gasar zai samu damar yin ziyarar mako guda kyauta a tsibiran Malvinas.

Game da hakan, ma’aikatar harkokin wajen kasar Argentina, ta fitar da sanarwar nuna rashin jin dadin ta, inda ta ce, matakin da Birtaniya ta dauka na nufin cewa tana mallakar tsibiran, don haka ta bukaci Birtaniya da ta cika alkawarin da ta dauka karkashin kudurin MDD, kana ta yi shawarwari da Argentina game da ikon mulkin tsibiran.

  • Kasar Sin Ta Lashi Takwabin Kare Ikonta Bayan Ziyarar Da ‘Yan Majalisar Amurka Suka Kai Yankin Taiwan

A shekarar 1816, Argentina ta samu ‘yanci daga mulkin mallakar kasar Spaniya, tare da samun ikon mulkin tsibiran Malvinas, amma lokacin da Birtaniya ta habaka mulkin mallakarta a kudancin nahiyar Amurka, ta mamaye tsibiran na Malvinas a shekarar 1833.

A shekarar 1982, yakin da aka gwabza na tsawon kwanaki 74 tsakanin kasashen biyu, domin karbe ikon mulkin tsibiran, ya kai ga Birtaniya ta samun nasara. Amma duk da haka, Argentina ba ta taba yi watsi da ikon mulkin tsibiran ba.

Kwamitin hana mulkin mallaka na MDD, ya fitar da kuduri har fiye da sau 30, don kalubalantar gwamnatin Birtaniya, da Argentina, da su yi shawarwari kan batun, kuma sau da dama Argentina ta gaggayci Birtaniya da ta shiga shawarwari, amma Birtaniya ta ki karbar gayyatar.

Labarai Masu Nasaba

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Birtaniya ba za ta canja ikon mulkin tsibiran ba, saboda shaiddu da ake da su game da batun, duk da atisayen soja, ko na makamai da take girkewa, ko gasar da za ta gudanar da sauransu ba.

A watan Maris na shekarar 2016, kwamitin tabbatar da iyakokin bangarorin duniya na MDD, ya ba da tabbacin cewa, Argentina na da ikon mulkin tsibiran Malvinas.

Ban da wannan kuma, kimanin dukkan kasashe dake nahiyar Latin Amurka, da yankin Caribbean, suna goyon bayan Argentina game da batun. Kaza lika ita ma kasar Sin tana marawa Argentina baya, kan ikon mulkin tsibiran. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Wa Mawaki Eedris Abdulkareem Dashen Koda

Next Post

A Karon Farko Gwamnatin Kano Za Ta Nada Matashi Mai Karancin Shekaru Mukamin Kwamishina

Related

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

5 hours ago
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
Daga Birnin Sin

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

6 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

7 hours ago
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

8 hours ago
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
Daga Birnin Sin

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

9 hours ago
Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana

10 hours ago
Next Post
A Karon Farko Gwamnatin Kano Za Ta Nada Matashi Mai Karancin Shekaru Mukamin Kwamishina

A Karon Farko Gwamnatin Kano Za Ta Nada Matashi Mai Karancin Shekaru Mukamin Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

July 22, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

July 22, 2025
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.