ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Girmama Alkawarin Da Ta Dauka Game Da Batun Tsibiran Malvinas

by CMG Hausa
4 years ago
Birtaniya

Kwanan baya, ofishin jakadancin Birtaniya dake Argentina, ya gabatar da wata gasar bidiyo a kan yanar gizo, ga daliban jami’o’in dake kasar, inda ofishin ya yi ikirarin cewa, wanda ya lashe gasar zai samu damar yin ziyarar mako guda kyauta a tsibiran Malvinas.

Game da hakan, ma’aikatar harkokin wajen kasar Argentina, ta fitar da sanarwar nuna rashin jin dadin ta, inda ta ce, matakin da Birtaniya ta dauka na nufin cewa tana mallakar tsibiran, don haka ta bukaci Birtaniya da ta cika alkawarin da ta dauka karkashin kudurin MDD, kana ta yi shawarwari da Argentina game da ikon mulkin tsibiran.

  • Kasar Sin Ta Lashi Takwabin Kare Ikonta Bayan Ziyarar Da ‘Yan Majalisar Amurka Suka Kai Yankin Taiwan

A shekarar 1816, Argentina ta samu ‘yanci daga mulkin mallakar kasar Spaniya, tare da samun ikon mulkin tsibiran Malvinas, amma lokacin da Birtaniya ta habaka mulkin mallakarta a kudancin nahiyar Amurka, ta mamaye tsibiran na Malvinas a shekarar 1833.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1982, yakin da aka gwabza na tsawon kwanaki 74 tsakanin kasashen biyu, domin karbe ikon mulkin tsibiran, ya kai ga Birtaniya ta samun nasara. Amma duk da haka, Argentina ba ta taba yi watsi da ikon mulkin tsibiran ba.

Kwamitin hana mulkin mallaka na MDD, ya fitar da kuduri har fiye da sau 30, don kalubalantar gwamnatin Birtaniya, da Argentina, da su yi shawarwari kan batun, kuma sau da dama Argentina ta gaggayci Birtaniya da ta shiga shawarwari, amma Birtaniya ta ki karbar gayyatar.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Birtaniya ba za ta canja ikon mulkin tsibiran ba, saboda shaiddu da ake da su game da batun, duk da atisayen soja, ko na makamai da take girkewa, ko gasar da za ta gudanar da sauransu ba.

A watan Maris na shekarar 2016, kwamitin tabbatar da iyakokin bangarorin duniya na MDD, ya ba da tabbacin cewa, Argentina na da ikon mulkin tsibiran Malvinas.

Ban da wannan kuma, kimanin dukkan kasashe dake nahiyar Latin Amurka, da yankin Caribbean, suna goyon bayan Argentina game da batun. Kaza lika ita ma kasar Sin tana marawa Argentina baya, kan ikon mulkin tsibiran. (Amina Xu)

Birtaniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
A Karon Farko Gwamnatin Kano Za Ta Nada Matashi Mai Karancin Shekaru Mukamin Kwamishina

A Karon Farko Gwamnatin Kano Za Ta Nada Matashi Mai Karancin Shekaru Mukamin Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.