• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Waiwayi Tarihi Domin Daukar Darasi

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Birtaniya Ta Waiwayi Tarihi Domin Daukar Darasi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin wannan mako ne ake sa ran shugaban Tarayyar Turai, Charles Micheal, zai ziyarci kasar Sin, bisa gayyatar da shugaba Xi Jinping ya yi masa.

Wannan wani babban ci gaba ne a dangantakar dake tsakanin Sin da Turai, inda a karon farko, yawan cinikayya a tsakaninsu cikin shekarar da ta gabata, ya zarce dala biliyan 800, kana jari tsakanin bangarorin biyu, ya zarce dala biliyan 270.

  • An Bude Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka A Birnin Jinhua Na Kasar Sin

Lallai wannan ya shaida yadda cinikayya da kyakkyawar dangantaka tsakanin bangarorin biyu ke kyautata da kara farfadowa tare da haifar da dimbin sakamako da ribar moriyar juna.

Sai dai a daidai wannan lokaci ne kuma, aka jiyo sabon Firaministan Birtaniya Rishi Sunak, ya na wasu furuci da suka sauka daga kan turba, inda yake bayyana kasar Sin a matsayin barazana ga martaba da kimar kasashen yamma. Idan har ikirarin da yake yi gaskiya ne, ta yaya aka samu karuwar wadancan alkaluma na cinikayya tsakanin bangarorin biyu?

Tun da ya hau karagar mulki, ya ke bayyana kasar Sin a matsayin kalubale. Shin manufofin kasashen waje al’ummar Birtaniya suka damu da shi, ko kuma kyautatuwar zaman takewarsu?

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Firaministan na kaucewa ainihin alhakin da ya rataya a wuyansa na kula da al’umma da jagorantar kasarsa wajen samun ci gaba, inda yake mayar da hankali kan kasar Sin, wadda ba komai take nema ba, face zaman lafiya da hadin gwiwa da ci gaba na bai daya.

Ya kara da cewa, cinikayya tsakanin bangarorin biyu zai fuskanci sauye-sauye. An dai ga yadda Amurka ta tayar da rikicin cinikayya tsakaninta da Sin, kuma an ga gurguwar sakamakon da hakan ya haifar, inda ‘yan kasuwar kasar suka ji radadin a jikinsu.

Duniya na fuskantar tarin kalubale da suka hada da hauhawar farashin kayayyaki da masassarar tattalin arziki da yunwa da matsalar sauyin yanayi da makamashi, wadanda ba su bar kowacce kasa a baya ba. A wannan lokaci, kamata ya yi a hada hannu da ajiye bambance-bambance, wajen lalubo mafita tun kafin a rasa tudun dafawa.

Duk da wadannan kalubale dai, kasar Sin ta na kara daukar manufofin raya kanta da kyautata rayuwar al’ummarta, kuma cikin manufofin nata, har da kara fadada bude kofarta ga kasashen waje. Rufe kofa dai ko daukar ra’ayi na kashin kai ko kariyar cinikayya, sun riga sun shaida mana cewa, babu abun da suke haifarwa face koma baya. Kamata ya yi firaministan na Birtaniya, ya sake nazari ya waiwayi tarihi, ya kuma zame masa darasi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashen Sin Da Mongoliya Suna Hada Hannu Don Inganta Zamanintarwa A Sabon Zamani

Next Post

NAF Ta Kai Hari Sansanin Horar Da Dakarun ISWAP A Tafkin Chadi, Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 24

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

18 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

19 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

21 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

2 days ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

2 days ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

2 days ago
Next Post
NAF Ta Kai Hari Sansanin Horar Da Dakarun ISWAP A Tafkin Chadi, Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 24

NAF Ta Kai Hari Sansanin Horar Da Dakarun ISWAP A Tafkin Chadi, Ta Kashe 'Yan Ta'adda 24

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus ÆŠin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin ÆŠaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.