ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Waiwayi Tarihi Domin Daukar Darasi

by CMG Hausa
4 years ago
Birtaniya

A cikin wannan mako ne ake sa ran shugaban Tarayyar Turai, Charles Micheal, zai ziyarci kasar Sin, bisa gayyatar da shugaba Xi Jinping ya yi masa.

Wannan wani babban ci gaba ne a dangantakar dake tsakanin Sin da Turai, inda a karon farko, yawan cinikayya a tsakaninsu cikin shekarar da ta gabata, ya zarce dala biliyan 800, kana jari tsakanin bangarorin biyu, ya zarce dala biliyan 270.

  • An Bude Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka A Birnin Jinhua Na Kasar Sin

Lallai wannan ya shaida yadda cinikayya da kyakkyawar dangantaka tsakanin bangarorin biyu ke kyautata da kara farfadowa tare da haifar da dimbin sakamako da ribar moriyar juna.

ADVERTISEMENT

Sai dai a daidai wannan lokaci ne kuma, aka jiyo sabon Firaministan Birtaniya Rishi Sunak, ya na wasu furuci da suka sauka daga kan turba, inda yake bayyana kasar Sin a matsayin barazana ga martaba da kimar kasashen yamma. Idan har ikirarin da yake yi gaskiya ne, ta yaya aka samu karuwar wadancan alkaluma na cinikayya tsakanin bangarorin biyu?

Tun da ya hau karagar mulki, ya ke bayyana kasar Sin a matsayin kalubale. Shin manufofin kasashen waje al’ummar Birtaniya suka damu da shi, ko kuma kyautatuwar zaman takewarsu?

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Firaministan na kaucewa ainihin alhakin da ya rataya a wuyansa na kula da al’umma da jagorantar kasarsa wajen samun ci gaba, inda yake mayar da hankali kan kasar Sin, wadda ba komai take nema ba, face zaman lafiya da hadin gwiwa da ci gaba na bai daya.

Ya kara da cewa, cinikayya tsakanin bangarorin biyu zai fuskanci sauye-sauye. An dai ga yadda Amurka ta tayar da rikicin cinikayya tsakaninta da Sin, kuma an ga gurguwar sakamakon da hakan ya haifar, inda ‘yan kasuwar kasar suka ji radadin a jikinsu.

Duniya na fuskantar tarin kalubale da suka hada da hauhawar farashin kayayyaki da masassarar tattalin arziki da yunwa da matsalar sauyin yanayi da makamashi, wadanda ba su bar kowacce kasa a baya ba. A wannan lokaci, kamata ya yi a hada hannu da ajiye bambance-bambance, wajen lalubo mafita tun kafin a rasa tudun dafawa.

Duk da wadannan kalubale dai, kasar Sin ta na kara daukar manufofin raya kanta da kyautata rayuwar al’ummarta, kuma cikin manufofin nata, har da kara fadada bude kofarta ga kasashen waje. Rufe kofa dai ko daukar ra’ayi na kashin kai ko kariyar cinikayya, sun riga sun shaida mana cewa, babu abun da suke haifarwa face koma baya. Kamata ya yi firaministan na Birtaniya, ya sake nazari ya waiwayi tarihi, ya kuma zame masa darasi.

Birtaniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
NAF Ta Kai Hari Sansanin Horar Da Dakarun ISWAP A Tafkin Chadi, Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 24

NAF Ta Kai Hari Sansanin Horar Da Dakarun ISWAP A Tafkin Chadi, Ta Kashe 'Yan Ta'adda 24

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.