ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Waiwayi Tarihi Domin Daukar Darasi

by CMG Hausa
4 years ago
Birtaniya

A cikin wannan mako ne ake sa ran shugaban Tarayyar Turai, Charles Micheal, zai ziyarci kasar Sin, bisa gayyatar da shugaba Xi Jinping ya yi masa.

Wannan wani babban ci gaba ne a dangantakar dake tsakanin Sin da Turai, inda a karon farko, yawan cinikayya a tsakaninsu cikin shekarar da ta gabata, ya zarce dala biliyan 800, kana jari tsakanin bangarorin biyu, ya zarce dala biliyan 270.

  • An Bude Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka A Birnin Jinhua Na Kasar Sin

Lallai wannan ya shaida yadda cinikayya da kyakkyawar dangantaka tsakanin bangarorin biyu ke kyautata da kara farfadowa tare da haifar da dimbin sakamako da ribar moriyar juna.

ADVERTISEMENT

Sai dai a daidai wannan lokaci ne kuma, aka jiyo sabon Firaministan Birtaniya Rishi Sunak, ya na wasu furuci da suka sauka daga kan turba, inda yake bayyana kasar Sin a matsayin barazana ga martaba da kimar kasashen yamma. Idan har ikirarin da yake yi gaskiya ne, ta yaya aka samu karuwar wadancan alkaluma na cinikayya tsakanin bangarorin biyu?

Tun da ya hau karagar mulki, ya ke bayyana kasar Sin a matsayin kalubale. Shin manufofin kasashen waje al’ummar Birtaniya suka damu da shi, ko kuma kyautatuwar zaman takewarsu?

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Firaministan na kaucewa ainihin alhakin da ya rataya a wuyansa na kula da al’umma da jagorantar kasarsa wajen samun ci gaba, inda yake mayar da hankali kan kasar Sin, wadda ba komai take nema ba, face zaman lafiya da hadin gwiwa da ci gaba na bai daya.

Ya kara da cewa, cinikayya tsakanin bangarorin biyu zai fuskanci sauye-sauye. An dai ga yadda Amurka ta tayar da rikicin cinikayya tsakaninta da Sin, kuma an ga gurguwar sakamakon da hakan ya haifar, inda ‘yan kasuwar kasar suka ji radadin a jikinsu.

Duniya na fuskantar tarin kalubale da suka hada da hauhawar farashin kayayyaki da masassarar tattalin arziki da yunwa da matsalar sauyin yanayi da makamashi, wadanda ba su bar kowacce kasa a baya ba. A wannan lokaci, kamata ya yi a hada hannu da ajiye bambance-bambance, wajen lalubo mafita tun kafin a rasa tudun dafawa.

Duk da wadannan kalubale dai, kasar Sin ta na kara daukar manufofin raya kanta da kyautata rayuwar al’ummarta, kuma cikin manufofin nata, har da kara fadada bude kofarta ga kasashen waje. Rufe kofa dai ko daukar ra’ayi na kashin kai ko kariyar cinikayya, sun riga sun shaida mana cewa, babu abun da suke haifarwa face koma baya. Kamata ya yi firaministan na Birtaniya, ya sake nazari ya waiwayi tarihi, ya kuma zame masa darasi.

Birtaniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
NAF Ta Kai Hari Sansanin Horar Da Dakarun ISWAP A Tafkin Chadi, Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 24

NAF Ta Kai Hari Sansanin Horar Da Dakarun ISWAP A Tafkin Chadi, Ta Kashe 'Yan Ta'adda 24

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.