• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Yi Shawarwari Kan Ikon Mallakar Tsibiran Malvinas

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Birtaniya Ta Yi Shawarwari Kan Ikon Mallakar Tsibiran Malvinas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan nan ne ministan harkokin wajen kasar Birtaniya James Cleverly, ya bayyana cewa, kasarsa da kasar Mauritius, sun riga sun yanke shawarar gudanar da shawarwari kan batun da ya shafi ikon mallakar tsibiran Chagos, da sa ran cimma yarjejeniya a farkon shekara mai kamawa.

An maida irin wannan ra’ayin kasar Birtaniya, a matsayin wani muhimmin matakin da aka dauka, wajen daidaita rikicin ikon mallakar tsibiran Chagos.

  • Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

Tsibiran Chagos suna tsakiyar yankin ruwan tekun Indiya, yankuna ne da kasar Mauritius ta mallaka tun asali. A shekara ta 1965, a matsayin wani sharadin da aka gindayawa Mauritius don ta samu ‘yancin kai, kasar Birtaniya ta ware tsibiran Chagos daga Mauritius don su zama “yankunan dake karkashin mulkin Birtaniya a tekun Indiya”, ta kuma ce za ta mayar da su a lokacin da ya dace. Bayan da Mauritius ta samu ‘yancin kai a shekara ta 1968 har zuwa yanzu, ta dade da bukatar Birtaniya da ta maido mata da tsibiran.

Kamar batun da ya shafi tsibiran Chagos, batun tsibiran Malvinas, shi ma ya wakana ne a lokacin mulkin mallaka na kasar Birtaniya. A shekara ta 1816, kasar Argentina ta gaji ikon mallakar tsibiran Malvinas, bayan da ta samu ‘yancin kai daga mulkin mallakar kasar Sifaniya, amma Birtaniya ta dauki matakan soja, har ta kwace ikon mallakar tsibiran a shekara ta 1833.

A shekara ta 1965, an zartas da kudiri mai lamba 2065 a wajen babban taron Majalisar Dinkin Duniya, inda aka bukaci kasashen Birtaniya da Argentina, da su daidaita rikici ta hanyar shawarwari. Kana kuma, har sau sama da 30, kwamitin musamman na kawar da matsalar mulkin mallaka na MDD, ya zartas da kudirori don bukatar kasar Birtaniya ta yi shawarwari da kasar Argentina. Amma Birtaniya ta yi biris da haka.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Daga cikin yankuna 17 da har yanzu suke karkashin mulkin mallaka a duniya, akwai guda 10 dake karkashin mulkin Birtaniya. Ba rikicin ikon mallakar tsibiran Chagos kawai ya kamata ta warware ba, kamata ya yi ma ta gudanar da shawarwari tun da wuri tare da Argentina kan batun tsibiran Malvinas.

A wannan karnin da muke ciki, ra’ayin mulkin mallaka, da ra’ayin nuna babakere ba za su samu nasara ba. Dole ne kasar Birtaniya ta daidaita wadannan matsalolin tarihi yadda ya kamata! (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahaifi Ya Banka Wa ‘Ya’yan Matarsa 5 Wuta Kan Sabani Da Mahaifiyarsu A Ondo

Next Post

Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

4 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

21 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Birtaniya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.