• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Yi Shawarwari Kan Ikon Mallakar Tsibiran Malvinas

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Birtaniya Ta Yi Shawarwari Kan Ikon Mallakar Tsibiran Malvinas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan nan ne ministan harkokin wajen kasar Birtaniya James Cleverly, ya bayyana cewa, kasarsa da kasar Mauritius, sun riga sun yanke shawarar gudanar da shawarwari kan batun da ya shafi ikon mallakar tsibiran Chagos, da sa ran cimma yarjejeniya a farkon shekara mai kamawa.

An maida irin wannan ra’ayin kasar Birtaniya, a matsayin wani muhimmin matakin da aka dauka, wajen daidaita rikicin ikon mallakar tsibiran Chagos.

  • Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

Tsibiran Chagos suna tsakiyar yankin ruwan tekun Indiya, yankuna ne da kasar Mauritius ta mallaka tun asali. A shekara ta 1965, a matsayin wani sharadin da aka gindayawa Mauritius don ta samu ‘yancin kai, kasar Birtaniya ta ware tsibiran Chagos daga Mauritius don su zama “yankunan dake karkashin mulkin Birtaniya a tekun Indiya”, ta kuma ce za ta mayar da su a lokacin da ya dace. Bayan da Mauritius ta samu ‘yancin kai a shekara ta 1968 har zuwa yanzu, ta dade da bukatar Birtaniya da ta maido mata da tsibiran.

Kamar batun da ya shafi tsibiran Chagos, batun tsibiran Malvinas, shi ma ya wakana ne a lokacin mulkin mallaka na kasar Birtaniya. A shekara ta 1816, kasar Argentina ta gaji ikon mallakar tsibiran Malvinas, bayan da ta samu ‘yancin kai daga mulkin mallakar kasar Sifaniya, amma Birtaniya ta dauki matakan soja, har ta kwace ikon mallakar tsibiran a shekara ta 1833.

A shekara ta 1965, an zartas da kudiri mai lamba 2065 a wajen babban taron Majalisar Dinkin Duniya, inda aka bukaci kasashen Birtaniya da Argentina, da su daidaita rikici ta hanyar shawarwari. Kana kuma, har sau sama da 30, kwamitin musamman na kawar da matsalar mulkin mallaka na MDD, ya zartas da kudirori don bukatar kasar Birtaniya ta yi shawarwari da kasar Argentina. Amma Birtaniya ta yi biris da haka.

Labarai Masu Nasaba

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Daga cikin yankuna 17 da har yanzu suke karkashin mulkin mallaka a duniya, akwai guda 10 dake karkashin mulkin Birtaniya. Ba rikicin ikon mallakar tsibiran Chagos kawai ya kamata ta warware ba, kamata ya yi ma ta gudanar da shawarwari tun da wuri tare da Argentina kan batun tsibiran Malvinas.

A wannan karnin da muke ciki, ra’ayin mulkin mallaka, da ra’ayin nuna babakere ba za su samu nasara ba. Dole ne kasar Birtaniya ta daidaita wadannan matsalolin tarihi yadda ya kamata! (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahaifi Ya Banka Wa ‘Ya’yan Matarsa 5 Wuta Kan Sabani Da Mahaifiyarsu A Ondo

Next Post

Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

Related

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

17 minutes ago
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
Daga Birnin Sin

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

1 hour ago
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

2 hours ago
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

3 hours ago
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

4 hours ago
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

13 hours ago
Next Post
Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

LABARAI MASU NASABA

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara

August 7, 2025
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.