ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Kasar Sin

Koko daga kasar Ghana, shayi daga Kenya, Gahawa daga Habasha, zuma daga Zambia, barkono daga Rwanda……A cikin ’yan shekarun baya, karin kayayyakin kasashen Afirka na shiga kasuwannin kasar Sin, wadanda kuma suka samu karbuwa wurin al’ummar Sinawa.

A hakika, ba kayayyakin kasashen Afirka kadai ba, ingantattun kayayyaki daga fadin duniya na kara shiga kasuwannin kasar Sin cikin ’yan shekarun baya, wadanda baya ga biyan bukatun al’ummar kasar, sun kuma samar wa kasashen da ke fitar da kayayyakin damar cin gajiyar kasuwar kasar Sin mai matukar girma, kuma hakan na faruwa ne sakamakon yadda kasar Sin ke ta kara bude kofarta ga ketare.

  • Sin: Abubuwan Dake Cikin Rahoton Tsaron Amurka Na 2022 Game Da Sin Tsohon Tunani Ne Na Yakin Cacar Baka

Kwanan nan, an kaddamar da bikin baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin na kasa da kasa karo na biyar, ko CIIE a takaice, a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin. Bikin da aka fara kaddamar da shi a shekarar 2018, wanda kuma ya kasance baje koli na farko a duniya, dake da jigon kayayyakin da ake shigo da su daga kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

A gun bikin kaddamar da baje koli karo na biyar, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo, inda ya ce, yau shekaru biyar da suka wuce, na sanar da shirya bikin, da nufin kara bude kofar kasar Sin, ta yadda babbar kasuwar kasar Sin za ta kasance babbar dama ga duniya baki daya. Kididdiga ta nuna cewa, a wajen bukukuwan CIIE hudu da suka gabata, adadin kayayyakin da aka baje kolinsu ya kai dubu 270, kuma jimillar darajar yarjeniyoyin da aka daddale ta zarce dala biliyan 270, inda aka bullo da sabbin hajoji, da fasahohi, da hidimomi da yawansu ya wuce 1500. Bikin CIIE, tamkar dandali ne ga kasar Sin, na kafa sabon tsarin samar da ci gaba, da fadada bude kofarta ga kasashen ketare, inda sassan kasa da kasa za su ci gajiya tare.

A halin da ake ciki yanzu na fuskantar manyan sauye-sauye a duniya, da rashin karfin farfadowar tattalin arzikin duniya, shugaba Xi Jinping a jawabin da ya gabatar, ya yi nuni da cewa, bude wa juna kofa muhimmin mataki ne da zai tabbatar da ganin ci gaban dan Adam da bunkasuwar duniya, ya ce,“Ya dace mu kara bude kofarmu, don daidaita matsalolin ci gaba, da fadada hadin-gwiwa, da kara karfin yin kirkire-kirkire, da kuma samar da ci gaba tare, ta yadda za’a kara dunkule tattalin arzikin duniya baki daya, da samar da ci gaba ga kasa da kasa, don kara amfanar al’ummominsu cikin adalci”.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Duk da cewa ana fuskantar matsalolin kariyar ciniki da ra’ayi na kashin kai, amma kasar Sin ba ta taba daina kokarinta na kafa sabon tsarin tattalin arziki dake bude kofarta ga kasa da kasa ba. A cikin shekaru 10 da suka gabata, jimillar cinikayya a tsakanin Sin da kasashen duniya ya karu daga dala triliyan 4.4 zuwa triliyan 6.9, matakin da ya sa kasar Sin ta zamanto ta farko wajen yawan yin ciniki a duniya, da ma babbar abokiyar ciniki ga kasashe da shiyyoyi sama da 140.

Kaza lika kasar ta kuma rage matsakaicin kudin kwastam da ta sanya a kan kayayyakin da ta shigo da su daga kasa da kasa, zuwa kimanin kaso 7.4%, wato kasa da kaso 9.8% da ta alkawarta lokacin shiga kungiyar WTO, tare da cire kudin kwastam kan kaso 98% na kayayyakin da take shigowa daga wasu kasashe 16 da suka fi karancin ci gaba. Baya ga haka, matakan da ta dauka na haramta fannonin da ’yan kasuwan waje suke iya zubawa jari ma sun ragu daga 190 zuwa 27, raguwar da ta kai kaso 85%……

Jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin dake kan karagar mulkin kasar, a babban taron wakilanta karo na 20 da aka gudanar a kwanan baya, ta jaddada cewa, kasar Sin za ta tsaya tsayin daka a kan aiwatar da manufar bude kofarta ga kasashen waje, ta yadda kasar Sin za ta samar da damammaki ga duniya bisa ga ci gabanta, don kasashen duniya su ci gajiya.

A nan gaba, kasar Sin za ta kara bude kofarta, kuma kasar na son kasashen Afirka da ma sauran kasashen duniya su ci gajiyar damammakin da ake da su a babbar kasuwarta, da tsarinta na bude kofa da ma hadin gwiwar kasa da kasa. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 

 

 

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Mahaifi Ya Banka Wa ‘Ya’yan Matarsa 5 Wuta Kan Sabani Da Mahaifiyarsu A Ondo

Mahaifi Ya Banka Wa 'Ya'yan Matarsa 5 Wuta Kan Sabani Da Mahaifiyarsu A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.