ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Birtaniya Ta Yi Shawarwari Kan Ikon Mallakar Tsibiran Malvinas

by CMG Hausa
4 years ago
Birtaniya

A kwanan nan ne ministan harkokin wajen kasar Birtaniya James Cleverly, ya bayyana cewa, kasarsa da kasar Mauritius, sun riga sun yanke shawarar gudanar da shawarwari kan batun da ya shafi ikon mallakar tsibiran Chagos, da sa ran cimma yarjejeniya a farkon shekara mai kamawa.

An maida irin wannan ra’ayin kasar Birtaniya, a matsayin wani muhimmin matakin da aka dauka, wajen daidaita rikicin ikon mallakar tsibiran Chagos.

  • Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

Tsibiran Chagos suna tsakiyar yankin ruwan tekun Indiya, yankuna ne da kasar Mauritius ta mallaka tun asali. A shekara ta 1965, a matsayin wani sharadin da aka gindayawa Mauritius don ta samu ‘yancin kai, kasar Birtaniya ta ware tsibiran Chagos daga Mauritius don su zama “yankunan dake karkashin mulkin Birtaniya a tekun Indiya”, ta kuma ce za ta mayar da su a lokacin da ya dace. Bayan da Mauritius ta samu ‘yancin kai a shekara ta 1968 har zuwa yanzu, ta dade da bukatar Birtaniya da ta maido mata da tsibiran.

ADVERTISEMENT

Kamar batun da ya shafi tsibiran Chagos, batun tsibiran Malvinas, shi ma ya wakana ne a lokacin mulkin mallaka na kasar Birtaniya. A shekara ta 1816, kasar Argentina ta gaji ikon mallakar tsibiran Malvinas, bayan da ta samu ‘yancin kai daga mulkin mallakar kasar Sifaniya, amma Birtaniya ta dauki matakan soja, har ta kwace ikon mallakar tsibiran a shekara ta 1833.

A shekara ta 1965, an zartas da kudiri mai lamba 2065 a wajen babban taron Majalisar Dinkin Duniya, inda aka bukaci kasashen Birtaniya da Argentina, da su daidaita rikici ta hanyar shawarwari. Kana kuma, har sau sama da 30, kwamitin musamman na kawar da matsalar mulkin mallaka na MDD, ya zartas da kudirori don bukatar kasar Birtaniya ta yi shawarwari da kasar Argentina. Amma Birtaniya ta yi biris da haka.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Daga cikin yankuna 17 da har yanzu suke karkashin mulkin mallaka a duniya, akwai guda 10 dake karkashin mulkin Birtaniya. Ba rikicin ikon mallakar tsibiran Chagos kawai ya kamata ta warware ba, kamata ya yi ma ta gudanar da shawarwari tun da wuri tare da Argentina kan batun tsibiran Malvinas.

A wannan karnin da muke ciki, ra’ayin mulkin mallaka, da ra’ayin nuna babakere ba za su samu nasara ba. Dole ne kasar Birtaniya ta daidaita wadannan matsalolin tarihi yadda ya kamata! (Murtala Zhang)

Birtaniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.