• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Tunani Kan Laifinsu

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Tunani Kan Laifinsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya, gwamnatin soja ta jamhuriyar Nijar ta sanar da janye kasar daga kungiyar kasashe masu renon Faransa ko OIF. Hakan ya kasance wani sabon mataki da Nijar din ta dauka, da nufin yanke huldarta da kasar Faransa, wadda ta taba yin mulkin mallaka a kasar, bayan da aka janye jakadan Faransa, da sojojin kasar daga sassan kasar Nijar.

Hakika cikin shekaru 2 da suka gabata, an tilastawa kasar Faransa janye sojojinta daga kasashen Mali, da Afirka ta Tsakiya, da Burkina Faso, gami da Nijar, kana ra’ayin “kawar da abubuwa masu alaka da kasar Faransa”, na kara yaduwa cikin sauri a tsakanin kasashen yammacin Afirka da kasar Faransa ta taba musu mulki mallaka. Duk wadannan abubuwa sun nuna wani sabon yanayin da muke ciki ta fuskar siyasar kasa da kasa.

  • Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka
  • ‘Yan Sa-kai Za Su Taka Rawa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro A Arewacin Nijeriya – Yusha’u Kebbe

Dalilin da ya sa karin kasashen Afirka ke neman katse hulda da kasar Faransa shi ne kasar ta dade tana musu shisshigi, da ci da guminsu, amma ba tare da kawo tsaro da ci gaba ba.

A fannin tattalin arziki, kamfanonin kasar Faransa sun mallaki dimbin albarkatu masu muhimmanci a kasashen yammancin Afirka, kana kasar ta shawo kan tsare-tsaren hada-hadar kudi na kasashe 14 dake nahiyar Afirka, ta hanyar kafa yankin kudin Franc a Afirka. A fannin siyasa, kasar Faransa ta dade tana nuna goyon baya ga ’yan siyasar kasashen Afirka da suka taba karatu a kasar da kuma kishinta, da neman karkata manufofin kasashen Afirka zuwa ga alkiblar da take so, ta hanyar wasu matakan siyasa da na tattalin arziki. Kana ta fuskar aikin soja, kasar Faransa ta dade tana girke sojoji fiye da 5400 a yammacin Afirka. Tun daga shekarar 1962 har zuwa yanzu, ta yi shisshigi na soja a kalla karo 25 a nahiyar Afirka.

Sai dai duk wadannan matakai na shisshigi ba su haifar da ci gaban tattalin arizki a yammacin Afirka ba. A wannan yanki, har zuwa yanzu, akwai kasashe 10 da kasar Faransa ta taba musu mulkin mallaka, wadanda ke cikin jerin sunayen kasashe mafi raunin tattalin arziki a duniya. Ban da haka, ayyukan ta’addanci na ta karuwa a yankin Sahel dake yammacin Afirka. An ce, a shekarar 2022, yawan mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren ta’addanci a yankin ya kai kashi 43% na jimillar mutanen da suka mutu sakamakon wannan dalili a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

A nasu bangare, mutanen kasar Faransa sun fara tunani kan laifin kansu, ganin yadda ake kin jininsu a nahiyar Afirka. A karshen shekarar bara, majalisun dokokin kasar Faransa sun gabatar da wani rahoto, wanda ya bukaci gwamnatin kasar da ta samar da karin tallafi ga kasashen Afirka, da daukar nagartattun matakai masu amfani, da nuna dukkan bayanai a fili a nahiyar Afirka.

Wasu kafofin watsa labaru na kasar sun ma ce, “Ya kamata a canza salon huldar dake tsakanin kasar Faransa da kasashen Afirka, wadda ta yi kama da ta baba da yara.”
Ban da haka, kasar Birtaniya ma ta fara tunanin laifinta. A shafin yanar gizo ko Internet, kamfanin BBC ya nuna wani bayani mai taken “Me ya sa kasashen yamma ba su ji dadi a shekarar 2023 ba?”, inda aka ce, cikin shekara daya da ta gabata, Amurka, da kasashen Turai, da sauran manyan kasashe masu bin tsarin “Dimokuradiya”, sun gamu da rashin nasara a dandamalin siyasar kasa da kasa. Marubucin wannan bayani ya ambaci yakin da ake yi tsakanin kasashen Rasha da Ukraine. Ya ce kasar Ukraine ba ta samu biyan bukata sosai ba a yakin da take yi da kasar Rasha, wanda ya nuna mawuyacin halin da kasar Amurka da kasashen Turai suke ciki, wadanda suka riga suka samar da kudin tallafi da ya kai dalar Amurka fiye da biliyan gomai ga Ukraine din.

Ban da haka, an ce, ko da yake kasashen yamma na Allah wadai da hare-haren da kasar Rasha take kaddamarwa, a hannu guda, sauran kasashen na da ra’ayi na daban. A ganin dimbin kasashen, habakar kungiyar tsaro ta NATO zuwa yankin gabas ya tsokani kasar Rasha, abin da ya ta da yaki daga bisani.

Har ila yau, cikin bayanin da kamfanin BBC ya gabatar, an tabo maganar yakin da ya barke tsakanin Falasdinu da Isra’ila, wanda shi ma ya karya kwarjinin kasashen yamma. An ce wannan yaki ya karkata hankalin mutanen duniya daga kan abokiyar kungiyar NATO, wato Ukraine. Kana wanda ya fi muhimmanci shi ne, a ganin dimibin Musulmai da sauran gungun mutane na kasashe daban daban, yadda kasashen Amurka da Birtaniya ke neman kare kasar Isra’ila a MDD, ya nuna cewa su ma suna da jini a hannunsu, a kisan kiyashi da aka yi wa dubun-dubatar jama’ar yankin Gaza, wadanda ba su san hawa ba, balle ma sauka.
Kamar dai yadda Hausawa su kan ce, jiki magayi ne. Mutanen kasashen yamma ba za su fadi gaskiya ba, har sai sun gamu da matsala. Sai dai yadda kasashen yamma ke fama da mawuyacin hali a wurare daban daban, ya nuna bambancin da aka samu, tsakanin yadda kasashen yamma suke kallon kansu da ainihin abubuwan da suke iya yi, gami da tsakanin ra’ayin su kan abubuwa, da kuma tunani mafi samun farin jini a duniya.

Saboda haka, kamata ya yi, kasashen yamma su kara tunani kan laifukansu, don magance aikata karin laifuka, da baiwa kasashen duniya karin damammaki na samun ci gaba, ta hanyar tabbatar da zaman lafiya, da gudanar da hadin kai mai amfani ga kowa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JapanKasar SinTaiwan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Sin Ya Bunkasa Sashen Sabbin Makamashi A Zimbabwe

Next Post

Jerin Jami’o’i 18 Da NUC Ta Haramta Karatu Acikinsu

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

12 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

13 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

14 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

15 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

16 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

18 hours ago
Next Post
NUC

Jerin Jami'o'i 18 Da NUC Ta Haramta Karatu Acikinsu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.