• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Tunani Kan Laifinsu

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Tunani Kan Laifinsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya, gwamnatin soja ta jamhuriyar Nijar ta sanar da janye kasar daga kungiyar kasashe masu renon Faransa ko OIF. Hakan ya kasance wani sabon mataki da Nijar din ta dauka, da nufin yanke huldarta da kasar Faransa, wadda ta taba yin mulkin mallaka a kasar, bayan da aka janye jakadan Faransa, da sojojin kasar daga sassan kasar Nijar.

Hakika cikin shekaru 2 da suka gabata, an tilastawa kasar Faransa janye sojojinta daga kasashen Mali, da Afirka ta Tsakiya, da Burkina Faso, gami da Nijar, kana ra’ayin “kawar da abubuwa masu alaka da kasar Faransa”, na kara yaduwa cikin sauri a tsakanin kasashen yammacin Afirka da kasar Faransa ta taba musu mulki mallaka. Duk wadannan abubuwa sun nuna wani sabon yanayin da muke ciki ta fuskar siyasar kasa da kasa.

  • Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka
  • ‘Yan Sa-kai Za Su Taka Rawa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro A Arewacin Nijeriya – Yusha’u Kebbe

Dalilin da ya sa karin kasashen Afirka ke neman katse hulda da kasar Faransa shi ne kasar ta dade tana musu shisshigi, da ci da guminsu, amma ba tare da kawo tsaro da ci gaba ba.

A fannin tattalin arziki, kamfanonin kasar Faransa sun mallaki dimbin albarkatu masu muhimmanci a kasashen yammancin Afirka, kana kasar ta shawo kan tsare-tsaren hada-hadar kudi na kasashe 14 dake nahiyar Afirka, ta hanyar kafa yankin kudin Franc a Afirka. A fannin siyasa, kasar Faransa ta dade tana nuna goyon baya ga ’yan siyasar kasashen Afirka da suka taba karatu a kasar da kuma kishinta, da neman karkata manufofin kasashen Afirka zuwa ga alkiblar da take so, ta hanyar wasu matakan siyasa da na tattalin arziki. Kana ta fuskar aikin soja, kasar Faransa ta dade tana girke sojoji fiye da 5400 a yammacin Afirka. Tun daga shekarar 1962 har zuwa yanzu, ta yi shisshigi na soja a kalla karo 25 a nahiyar Afirka.

Sai dai duk wadannan matakai na shisshigi ba su haifar da ci gaban tattalin arizki a yammacin Afirka ba. A wannan yanki, har zuwa yanzu, akwai kasashe 10 da kasar Faransa ta taba musu mulkin mallaka, wadanda ke cikin jerin sunayen kasashe mafi raunin tattalin arziki a duniya. Ban da haka, ayyukan ta’addanci na ta karuwa a yankin Sahel dake yammacin Afirka. An ce, a shekarar 2022, yawan mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren ta’addanci a yankin ya kai kashi 43% na jimillar mutanen da suka mutu sakamakon wannan dalili a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

A nasu bangare, mutanen kasar Faransa sun fara tunani kan laifin kansu, ganin yadda ake kin jininsu a nahiyar Afirka. A karshen shekarar bara, majalisun dokokin kasar Faransa sun gabatar da wani rahoto, wanda ya bukaci gwamnatin kasar da ta samar da karin tallafi ga kasashen Afirka, da daukar nagartattun matakai masu amfani, da nuna dukkan bayanai a fili a nahiyar Afirka.

Wasu kafofin watsa labaru na kasar sun ma ce, “Ya kamata a canza salon huldar dake tsakanin kasar Faransa da kasashen Afirka, wadda ta yi kama da ta baba da yara.”
Ban da haka, kasar Birtaniya ma ta fara tunanin laifinta. A shafin yanar gizo ko Internet, kamfanin BBC ya nuna wani bayani mai taken “Me ya sa kasashen yamma ba su ji dadi a shekarar 2023 ba?”, inda aka ce, cikin shekara daya da ta gabata, Amurka, da kasashen Turai, da sauran manyan kasashe masu bin tsarin “Dimokuradiya”, sun gamu da rashin nasara a dandamalin siyasar kasa da kasa. Marubucin wannan bayani ya ambaci yakin da ake yi tsakanin kasashen Rasha da Ukraine. Ya ce kasar Ukraine ba ta samu biyan bukata sosai ba a yakin da take yi da kasar Rasha, wanda ya nuna mawuyacin halin da kasar Amurka da kasashen Turai suke ciki, wadanda suka riga suka samar da kudin tallafi da ya kai dalar Amurka fiye da biliyan gomai ga Ukraine din.

Ban da haka, an ce, ko da yake kasashen yamma na Allah wadai da hare-haren da kasar Rasha take kaddamarwa, a hannu guda, sauran kasashen na da ra’ayi na daban. A ganin dimbin kasashen, habakar kungiyar tsaro ta NATO zuwa yankin gabas ya tsokani kasar Rasha, abin da ya ta da yaki daga bisani.

Har ila yau, cikin bayanin da kamfanin BBC ya gabatar, an tabo maganar yakin da ya barke tsakanin Falasdinu da Isra’ila, wanda shi ma ya karya kwarjinin kasashen yamma. An ce wannan yaki ya karkata hankalin mutanen duniya daga kan abokiyar kungiyar NATO, wato Ukraine. Kana wanda ya fi muhimmanci shi ne, a ganin dimibin Musulmai da sauran gungun mutane na kasashe daban daban, yadda kasashen Amurka da Birtaniya ke neman kare kasar Isra’ila a MDD, ya nuna cewa su ma suna da jini a hannunsu, a kisan kiyashi da aka yi wa dubun-dubatar jama’ar yankin Gaza, wadanda ba su san hawa ba, balle ma sauka.
Kamar dai yadda Hausawa su kan ce, jiki magayi ne. Mutanen kasashen yamma ba za su fadi gaskiya ba, har sai sun gamu da matsala. Sai dai yadda kasashen yamma ke fama da mawuyacin hali a wurare daban daban, ya nuna bambancin da aka samu, tsakanin yadda kasashen yamma suke kallon kansu da ainihin abubuwan da suke iya yi, gami da tsakanin ra’ayin su kan abubuwa, da kuma tunani mafi samun farin jini a duniya.

Saboda haka, kamata ya yi, kasashen yamma su kara tunani kan laifukansu, don magance aikata karin laifuka, da baiwa kasashen duniya karin damammaki na samun ci gaba, ta hanyar tabbatar da zaman lafiya, da gudanar da hadin kai mai amfani ga kowa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JapanKasar SinTaiwan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Sin Ya Bunkasa Sashen Sabbin Makamashi A Zimbabwe

Next Post

Jerin Jami’o’i 18 Da NUC Ta Haramta Karatu Acikinsu

Related

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60
Daga Birnin Sin

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

45 minutes ago
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

21 hours ago
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

22 hours ago
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
Daga Birnin Sin

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

23 hours ago
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

24 hours ago
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

2 days ago
Next Post
NUC

Jerin Jami'o'i 18 Da NUC Ta Haramta Karatu Acikinsu

LABARAI MASU NASABA

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

August 5, 2025
Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

August 5, 2025
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.