• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Mu Dore Da Ibadu Da Kyawawan Halayenmu Na Ramadan

by Ibrahim Bala
2 years ago
Ibadu

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanku da sallah da fatan an yi sallah lafiya kuma an gabatar da ibadu cikin nutsuwa da yadda ubangiji ya tsara a yi.

Maganar da zan yi a yau, magana ce guda daya wadda take shawara ce gare ku ‘yan’uwa, kamar yadda muka gabatar da ibadu a cikin watan Ramadana za a ga karya ta ragu, gulma da munafunci duk an kiyaye baki, saboda a tsira kuma a samu falala mai yawa, an kyautata zumunci, kuma an nemi yafiya an gafartawa juna.

Shawarata a nan ita ce; wannan wata mai alfarma da muka yi ibadu cikinsa, ya zamanto an dore kowane wata a cikin shekara watanninmu goma sha biyu, mu yi irin wadannan ibadun mu yi koyi, ya zamanto idan wani abu a ke yi na zunubi ko na wani laifi da a ka daina a watan ramadan to, a dore da shi.

In Allah ya so ya yarda za mu ga budi, mu ga falala, kada ka ce idan watan ramadan ya riga ya wuce ya kare ai shikkenan za ka ci gaba da ayyukan da ka saba yi na laifuka tunda wata ya riga ya kare, a’a! a kiyaye domin samun tsira ranar gobe kiyama.

LABARAI MASU NASABA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

Ina mai kara bawa ‘yan’uwa shawara kan cewa; Dan Allah dan Annabi darussan da muka gani a watan ramadana mu dore da su, mun kyautata, mun yi sadaka, mun taimaki marayu, mun yi ibada, mun yi sallolin dare, to mu dore, mu daure, mu ci gaba da su, za mu ga canji, kuma za mu ga ci gaba.

Ina kara kira ga iyaye yadda suka rika saka ‘ya’yansu suka rika yin ibadu na dare da yin sallah a kan lokaci saboda azumi to ya kamata a dore a hakan, kada a ce sai lokacin azumi za a yi ibada, kada ka ce sai lokacin azumi kawai za ka tashi ‘ya’yanka a yi sallar asubha, a yi sallar dare, a roki Allah subhanahu wata’allah, to a dore a haka.

Haka kuma ina kara kira ga ‘yan’uwa musulmi akwai sittisshawwal falala ce mai girma a wannan azumin duk da cewa ni ba malami bane amma ina ba mu shawara da mu daure mu yi su, zai taimaka mana, kuma zai cike mana irin laifukan da muke da su na lada da muke nema.

Ubangiji Allah ya karbi ibadunmu, Amin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

December 29, 2024
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

December 21, 2024
Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
Marurun Zuciya

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

May 12, 2024
Next Post
Yanzu-yanzu: Hatsaniya Ta Kaure Tsakanin Sojoji Da Matasa A Gashuwa

Yanzu-yanzu: Hatsaniya Ta Kaure Tsakanin Sojoji Da Matasa A Gashuwa

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.