• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kimar Mace Mara Sana’a Take A Wurin Mijinta?

by Amina Usman
2 years ago
in Sana'a Sa'a
0
Ya Kimar Mace Mara Sana’a Take A Wurin Mijinta?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk sanda akace mutum yana da dan abun juyawa duk kankantar sa tabbas ya karawa kansa kima sannan ya ragewa kansa damuwa.

Mace mau sana’a ko a wurin dangin miji kimarta daban take balle kuma akai ga shi kanshi mijin.

  • Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu
  • Li Keqiang Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Firaministan Equatorial Guinea

To idan kuma uwargida ta maida kanta sai anci an bata to fa tabbas ta hadu da aikin jira dan kuwa duk yanda kike so kiyiwa kanki abu dole ki hakura sai an dauko an baki.

Kamar yadda aka sani uwargidan da batada kwakwarar sana’a adinga inda kaganta zaka tafita daban acikin tsara,kuma rashin dan na kashewa yana janyo abubuwa da Dama musamman a zamantakewar aure.

Abu na farko mace mara sana’a zata kasance kullum cikin kunci bata san me ke mata dadi ba musamman ma idan mijin ba mai hali ba ne sosai,zata kasance ko zamantakewar ta da miji ma babu dadi kawai sai taji tana jin haushin shi batare da yayi mata wani kwakwaran laifi ba .

Labarai Masu Nasaba

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

Rashin sana’a na sa uwar gida ko acikin danginta ta zama mujiya ta koma kamar bare,sai abinda akaci aka bata ,ko shawara za ayi sai taga ana damawa kannenta masu dan abun hannun su amma ita kuwa ta zama bare.

Hakazalika rashin abin yi na sa uwargida ta zama ‘Depressed’ wato ta kasance cikin kuci ba tada walwala. Amma yau in uwargida zata samu dan abin juyawa zata kasance batada lokaci zama tayi tunanin banza ba lokacin ta zai kasance na juya taro ya koma sisi ne.

Kamar yadda mawakiya Barmani Choge ta ke kirari a wakarta inda take cewa ‘a kama sana’a mata zaman banza ba namu ba’ to wannan magana haka take .Uwargida in kika kama sana’a ke kanki zakiji kin fi samun natsuwa yan kananan hidimar ki ba sai kin jira miji ya zo ya miki ba.

Haka yara zaki taimakawa maigida da dan kanana hidimansu wanda dai baifi karfin ki ba, kuma ko su kansu yaran sun san ana musu in suna da dan bukatun su zakiga sun nufo ki amma ba wai in sunzo sun ce a basu kusin fensir ba ki ce to ku jira Baban ku ya dawo .Wannan yana rage daraja har a idon maigida.

Uwagidan da ta rike sana’a ko shi kanshi mijin yanda zai mata magana cikin fahimta daban ne da wacce take zaune zai an daga sai an tayar. In uwargida na juya biyar ta koma goma za taga yanayin zaman lafiya a gidan ma ya karu babu yawan gaba,babu yawan jin haushin juna ko kuma hantara.

Sana’a nasa miji ya kalle mace da daraja sa kuma kima saboda yawan bani bani ko a gidan ku ne yana jawo raini amma in kika kasance kina dan daukewa maigida wasu nauyi to fa duk duniya babu kamar ki.

Koda ace uwar gida tana hidima mijin baya nuna halin ko in kula yanuna kamar bai sani ba to fa cikin ransa ba karamin farin cikin yake yi ba dan yasan dole akwai kina dauke masa wasu tallafi.

Mata a gyara a rage zaman banza, a nemi sana’a akwai sana’o’i iri daban daban kala kala sai wanda kika zaba kamar su Dinki,turaren wuta, saida itace,saka,da dai sauran su kuma duk wanda uwar gida tasa kai zata iya kuma zata samu alheri sosai dan ta tallafawa kanta har ma da ‘yan uwanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KimaMataMijiSana"a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zai Yiwu A Samu Hadarin Kaucewar Jiragen Kasa Da Yawa Daga Kan Layin Dogo A Lokaci Guda Ba

Next Post

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Musanta Bai Wa Bankuna Umarnin Karbar Tsoffin Kudi

Related

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera
Sana'a Sa'a

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera

5 months ago
Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi
Labarai

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

7 months ago
Akwai Dimbin Alhairi A Harkar Kasuwanci Na Kirifto – Khadija Ahmad
Labarai

Akwai Dimbin Alhairi A Harkar Kasuwanci Na Kirifto – Khadija Ahmad

10 months ago
Dangote Ya Soki Sabon Tsarin Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Dangote Ya Soki Sabon Tsarin Gwamnatin Tinubu

12 months ago
Shara
Sana'a Sa'a

Sarrafa Daskararriyar Shara

2 years ago
Halin Da Masu Kananan Sana’o’i Ke Ciki (3)
Sana'a Sa'a

Halin Da Masu Kananan Sana’o’i Ke Ciki (3)

2 years ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: CBN Ya Musanta Bai Wa Bankuna Umarnin Karbar Tsoffin Kudi

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Musanta Bai Wa Bankuna Umarnin Karbar Tsoffin Kudi

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.