• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara

by Sadiq
3 years ago
in Al'ajabi
0
Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dubun wani mutum ta cika bayan da aka cafke shi yana sayar wa mutane garin katako da siminti a matsayin maganin gargajiya.

Wata majiya ta rawaito cewa ‘yansanda sun gano mutumin yana hada garin katako da garin farin simintin inda yake sayar wa mutane a matsayin maganin ciwon zazzabin cizon sauro da sauransu.

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsohon Atoni-Janar Na Legas Bisa Laifin Karkatar Da Kudade
  • Gwamnatin Tarayya Ta Shiga Tsakani Kan Rikicin Da Ya Kunno Kai Tsakanin Gwamnatin Kogi Da Dangote

A wani bidiyon da aka yi wa mutumin bayan ya shiga hannu, ya ce “Garin katako nake hadawa da garin siminti da kuma garin gypsum da ake yin POP da shi nake kullawa a leda ina sayar wa mutane a matsayin maganin cutar maleriya da sauran cututtuka.

“Ina zuwa kasuwanni daban-daban ina sayarwa kuma mutane suna yawan saya.

“Ba ni da kayyadajjen farashin da nake sayarwa, kawai ya danganta da yadda ciniki ya kaya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

“Na san yana da hatsari, amma saboda yanayin matsayin rayuwar da kasa ke ciki shi ya sa nake yin hakan.”

Wata mata mai suna Taibat, da ke zaune a unguwar Gerewu, ta ce wanda ake zargin yana yawan zuwa kasuwar Mandate da ke Ilori yana sayar da garin, kafin dubunsa ta cika.

Taibat, ta yi kira ga jama’a da su kara lura, sannan ta bukaci gwamnati ta dauki kwararan matakai, inda ta ce Allah ne kadai ya san irin lahanin da garin maganin ya yi wa mutanen da suka yi amfani da shi.

Sai dai kakakin ’yansandan Jihar Kwara, Ajayi Okasanmi, ya ce ba shi da labarin faruwar lamarin.

Amma duk da haka, kakakin ’yansandan ya ce da zarar an sanar da ’yansanda za su dauki mataki.

Idan ba a manta ba a baya-bayan nan hukumar NAFDAC sai da ta yi gargadi kan amfani da wasu magaunguna musamman wanda suke da alaka da gargajiya, inda ta ce suna da hatsari ga lafiyar mutane.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaGarin KatakoIlorinKwaraMaganin GargajiyaSiminti
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Gurfanar Da Tsohon Atoni-Janar Na Legas Bisa Laifin Karkatar Da Kudade

Next Post

Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku

Related

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

1 week ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

1 week ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

3 weeks ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

2 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

3 months ago
Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja
Al'ajabi

Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja

4 months ago
Next Post
Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku

Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.