• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara

by Sadiq
3 years ago
Maganin Gargajiya

Dubun wani mutum ta cika bayan da aka cafke shi yana sayar wa mutane garin katako da siminti a matsayin maganin gargajiya.

Wata majiya ta rawaito cewa ‘yansanda sun gano mutumin yana hada garin katako da garin farin simintin inda yake sayar wa mutane a matsayin maganin ciwon zazzabin cizon sauro da sauransu.

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsohon Atoni-Janar Na Legas Bisa Laifin Karkatar Da Kudade
  • Gwamnatin Tarayya Ta Shiga Tsakani Kan Rikicin Da Ya Kunno Kai Tsakanin Gwamnatin Kogi Da Dangote

A wani bidiyon da aka yi wa mutumin bayan ya shiga hannu, ya ce “Garin katako nake hadawa da garin siminti da kuma garin gypsum da ake yin POP da shi nake kullawa a leda ina sayar wa mutane a matsayin maganin cutar maleriya da sauran cututtuka.

“Ina zuwa kasuwanni daban-daban ina sayarwa kuma mutane suna yawan saya.

“Ba ni da kayyadajjen farashin da nake sayarwa, kawai ya danganta da yadda ciniki ya kaya.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

“Na san yana da hatsari, amma saboda yanayin matsayin rayuwar da kasa ke ciki shi ya sa nake yin hakan.”

Wata mata mai suna Taibat, da ke zaune a unguwar Gerewu, ta ce wanda ake zargin yana yawan zuwa kasuwar Mandate da ke Ilori yana sayar da garin, kafin dubunsa ta cika.

Taibat, ta yi kira ga jama’a da su kara lura, sannan ta bukaci gwamnati ta dauki kwararan matakai, inda ta ce Allah ne kadai ya san irin lahanin da garin maganin ya yi wa mutanen da suka yi amfani da shi.

Sai dai kakakin ’yansandan Jihar Kwara, Ajayi Okasanmi, ya ce ba shi da labarin faruwar lamarin.

Amma duk da haka, kakakin ’yansandan ya ce da zarar an sanar da ’yansanda za su dauki mataki.

Idan ba a manta ba a baya-bayan nan hukumar NAFDAC sai da ta yi gargadi kan amfani da wasu magaunguna musamman wanda suke da alaka da gargajiya, inda ta ce suna da hatsari ga lafiyar mutane.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Next Post
Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku

Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.